Manyan Labarai A Yau
Wani shugaban al'umma ya naushi Sarki mai masaukin baƙi a wurin taron da gwamna ya kaddamar da aikin titi, lamarin ya faru ne daga an ce mutum ya canza wuri.
Tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha, ya fito ya ƙaryata jita-jitar da ke cewa yana shirin ficewa daga jam'iyyar APC. Ya ce yana nan zama daram.
Babban kusa a jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya, Segun Showunmi, ya bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya gwamnoni sakarwa kananan hukumomi mara.
Wasu 'yan daba dauke da makamai sun kai farmaki kan wani ofishin hukumar NSCDC da ke jihar Kano. Sun kai harin ne bayan an kashe wani mai satar waya.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince a biya ma'aikata da 'yan fansho kudade don su gudanar da bukukuwan babbar Sallah a cikin walwala da jindadi.
Gwamnatin jihar Yobe karkashin jagorancin gwamna Mai Mala Buni ta ba da hutun kwanaki 10 ga makarantun sakandire da na firamare saboda zuwan sallah.
Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bukaci 'yan Arewa da su marawa shugaban kasa, Bola Tinubu baya a zaben 2027. Ya ce hakan shi ne adalci.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa babu wanda ya isa ya kore shi daga jam'iyyar PDP. Ya ce zai kuma ci gaba da zama a cikinta.
Babban malamin addinin Kirista kuma shugaban cocin INRI Evangelical Spirtual, Primate Elijah Ayodele, ya yabi shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Ya ce ya fi Buhari.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari