Manyan Labarai A Yau
Zafin rana ya haddasa cinikin ORS a Kano yayin azumi. Jama’a na amfani da shi don hana gajiya, amma likitoci sun gargadi cewa yawan shansa na iya haddasa matsaloli.
Karamar ministan harkokin wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta bayyana irin gwagwarmayar da ta sha a baya kafin ta kai matsayin da take a yanzu.
Wasu mutane daga mazabar Kogi ta Tsakiya sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da shirin da wasu ke yi na yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kiranye.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci kan 'yan sa-kai a jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun hallaka jami'an tsaro masu yawa a yayin harin.
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar SDP, Adewole Adebayo, ya nuna cewa ba za su shiga wata hadaka da APC ko wata jam'iyya ba. Ya ce SDP na da akidarta.
Kungiyar SERAP ta dauki matakin shari'a kan dakatarwar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Gwamna Siminalayi Fubara da 'yan majalisar dokokin Rivers.
Karamin ministan gidaje da ci gaban birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya taso Rabiu Musa Kwankwaso a gaba kan kalaman da ya yi dangane da dokar ta baci a Rivers.
Wani babban kusa a jam'iyyar PDP, Dan Orbih, ya tabo batun rawar da Nyesom Woke yake takawa a gwamnatin APC. Ya ce ministan Najeriya yake yi sa aiki.
Majalisar wakilai ta fito ta yi magana kan zargin da aka jefe ta da shi na karbar cin hanci kafin amincewa da bukatar Shugaba Bola Tinubu kan dokar ta baci a Rivers.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari