Manyan Labarai A Yau
Tankokin yakin Isra'ila sun bude wuta kan Falasdinawan da suka je wurin karbar abinci a zirin Gaza. An samu asarar rayuka sakamakon wutar da sojoji suka bude.
Sanata mai wakiltar Bayelsa ta Yamma a majalisar dattawan Najeriya, Seriake Dickson, ya bayyana gibin shugabanci a matakin kananan hukumomi na rura sashin tsaro.
Hukumomin ƙasar Isra'ila sun tabbatar da cewa an rufe matatar mai sakamakon rokokin da Iran ta sake harbawa yayin da rikicin ƙasashen ke ƙara ƙamari.
Gwamna Bala Mohanmed ya bayyana alhininsa bisa rasuwat iyan Jama'are kuma hakimin Hanifari, Ahmed Nuhu Wabi sakamakon hatsarin mota ranar Lahadi.
Mutane sama da 300,000 sun bar gidajensu bayan harin bama-baman da Isra'ila ta ƙara kaiwa birnin Tehran yayin da Iran ta nuna alamun amincewa da batun sulhu.
Gwamnatin jihar ta aika da sakon gargadi ga tubabbun 'yan bindigan da suka ajiye makamansu. Ta ce za su fuskanci hukunci idan suka saba alkawari.
Yan Majalisar dokokin kasar Iran sun kaɗa kuri'ar amincewa da Ali Madanizadeh a matsayin sabon ministan tattalin arziki da kudi don shawo kan matsalolinta.
Isra'ila ta farmaki gidan talabijin mallakin gwamnatin Iran a Tehran yayin watsa shirye-shirye. Iran ta yi Allah wadai da tare da yin kira ga MDD ta dauki mataki.
Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan Isra'ila, wanda ya kashe mutane takwas. Isra'ila ta gargadi mazauna Tehran da su fice daga garin, ta karya lagon Iran.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari