Manyan Labarai A Yau
Jigo a jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya nuna cewa babu wani yunkurin bata suna da zai hana Shugaba Bola Tinubu yin tazarce.
Gwamnatin jihar Kaduna ta yi martani mai zafi ga Nasir El-Rufai kan zarge-zargen da ya yi. Ta bayyana cewa ba za ta lamunci a kara jefa jihar cikin rikici ba.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki Peter Obi kan alkawarin da ya yi na yin shekara hudu kacal a kan mulki idan ya zama shugaban kasa.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bukaci tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya hakura da batun takara a zaben shekarar 2027.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya yi kalamai masu kaushi kan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi kira ga Peter Obi da Rotimim Amaechi kan alkawarin da suke yi dangane da yin wa'adin mulki na shekara hudu.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi zargin cewa gwamnati ce ta dauki nauyin 'yan daban da suka tarwatsa taron jam'iyyar ADC. Ya ce zai shigar da kara.
Gwamna Dikko Radda ya halarci jana'izar diyar sarkin Katsina, Khadijah Abdulmumin Kabir Usman, wacce ta rasu a Abuja. An ce Khadija ta rasu ta bar 'ya'ya uku.
Kungiyar All Progressives Media Network (APCMP) ta shawarci Goodluck Jonathan kan ka da ya yi takara da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari