Jihar Kano
Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya nuna alhininsa kan ambaliyar ruwan da ta auku a jihar Borno. Ya yi addu'ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.
A wannan rahoton, za ku ji cewa Attajirin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata ya ziyarci jihar Borno domin jajanta wa gwamnati da al'uma bisa iftila'in ambaliya.
Mai ba Abba Kabir Yusuf shawara ya ajiye mukami daga gwamnatin Kano ya koma APC. Sanata Barau Jibrin ya ce hakajn zai taimaka wajen kowo cigaba a APC.
A wannan labarin, mazauna unguwar Zango dake karamar hukumar Rimin-gado a Kano sun shiga tashin hankali bayan wani al'amari da ya afku a garin a ranar Asabar.
Ana zargin DSS da cin zarafin al'ummar Najeriya ba bisa ka'ida ba wanda ya zama ruwan dare kama daga mamayar ofishin SERAP zuwa cafke shugaban NLC, Joe Ajaero.
Gwamna Abba Yusuf ya jaddada cewa Kano tana tare da jihar Borno a mawuyacin halin da ta ke ciki na ambaliyar da ta mamaye Maiduguri. Abba ya ba da tallafin N100m.
Jam’iyyar adawa ta APC a Kano ta bayyana cewa za ta sa ido kan yadda gwamnatin Abba Kabir Yusuf za ta yi amfani da tallafin gwamnatin tarayya a jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa shugaban jam'iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya kaddamar shirin rabon tallafi ga matasa maza da mata na jihar Kano.
Abba wanda ɗa ne ga tsohon daraktan DSS, Yusuf Magaji Bichi ya ƙaryata jita-jitar da ake yadawa cewa ya dace kudin mahaifinsa har $2m inda ya ce karya ne.
Jihar Kano
Samu kari