Yaki da ta'addanci a Najeriya
Majalisar wakilan tarayya ta yi kira ga mai girma shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umurci jami'an tsaro su tashi tsaye a yaƙi da ƴan bindiga a jihar Katsina.
Wasu ƴan ta'adda da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram ke sun farmaki garin da ake sake ginawa ƴan gudun jira a karamar hukumar Dikwa ta jihar Borno.
Wasu mahara da ake kyautata zaton fulani makiyaya ne sun kashe dukkan iyalai yan gida ɗaya tare da ƙarin wasu da yawa a yankin ƙaramar hukumar Ukum, jihqr Benuwai.
Ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru, ya bayyana irin yadda rundunar sojojin Najeriya ke ci gaba da samun galaba kan masu tada ƙayar baya a faɗin kasar nan.
Tsagerun 'yan ta'addan Boko Haram sun yi awon gaba da mata 'yan gudun hijira har mutum 319 a wani sabok farmaki da suka kai a jihar Borno ta Najeriya.
Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun yi nasarar ceto mutane 15 daga hannun ƴan bindiga a kauyen Tsohuwar Tasha, ƙaramar hukumar Ƙaura Namoda.
Yan bindiga sun sake tare titin zuwa garin Maradun, hedkwatar ƙaramar hukumar Maradum a jihar Zamfara, sun yi ajalin babban jigon PDP tare da wasu bayin Allah.
Miyagun ƴan bindiga sun kai sabbin hare-hare kauyukan kananan hukumomi biyu a jihar Benuwai a karshen makon nan, sun kashe soja da wasu mutane da dama.
Gwamnatin jihar Borno ta ce zuwa yanzun manyan shugabannin kungiyar Boko Haram da suka kagoranci kafa ta a 2009 sun mutu ko sun miƙa wuya ga hukumomi.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari