Yaki da ta'addanci a Najeriya
Hedikwatar tsaro ta ce ta mika mutane 313 da ta kama ga gwamnatin Borno bisa umarnin babbar kotun tarayya da ke zamanta a Maiduguri. An gane mutanen ba su da laifi.
Asibitin kwararru na Reliance da ke Sokoto a ranar Laraba ya musanta cewa ya yi jinyar shugaban ‘yan bindiga Dogo Gide, wanda sojoji suka harbe shi.
Watanni kusan hudu bayan kuskuren jefa kan masu Maulidi a Kaduna, Gwamna Uba Sani ya fara ayyukan da ya yi alƙawari ga al'ummr kauyen Tudun Biri.
Tsohon ministan sadarwa, Adebayo Shittu, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta yi zaman sulhu da 'yan bindiga a yunkurinta na magance matsalar tsaro a Najeriya.
Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana rashin aikin yi a matsayin abin da ke kara ayyukan ta'addanci a Najeriya inda ya ce noma ce kadai za ta rage.
Farfesa Babagana Umaru Zulum ya ce shirin aminci a makarantu da suka kaddamar a Borno tun shekaru bakwai zuwa takwas da suka wuce yana aiki yadda ya kamata.
Wasu maharan sun yi garkuwa da matan aure 12 da namiji ɗaya, sun kwashi dukiyar bayin Allah mai ɗumbin yawa a karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina.
Rahotanni sun nuna cewa wasu gungun ƴan bindiga sun halaka dakaru 2 na rundunar CPG ta jihar Zamfara tare da ƙona motoci biyu a ƙaramar hukumar Tsafe.
Yayin da gwamnati ke zargin wasu da daukar nauyin ta'addanci, Tukur Mamu ya tsame kansa daga zargi inda ya ba gwamnati wa'adin kwana bakwai kan zarginsa da ta ke yi.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari