Gwamnatin tarayyar Najeriya
Kamfanin rarraba wutar lantarki watau TCN ya ce babu abin da ya ssmu babban layin wuta, layin Benin-Omotosho kawai ya ɗan samu matsala kuma ana kan gyara.
An fito da sabon salon GDP da zai rika la’akari da harkoki irinsu karuwanci. NBS tana so karfin tattalin arziki ya karu don haka za a tattaro sauran bangarori.
Karamar ministar kwadago, Nkeiruka Onyejeocha ta ce gwamnatin Tinubu za ta sake duba mafi ƙarancin albashin ma'aikata nan da ƙasa da shekaru biyu masu zuwa.
Reno Omokri ya bayyana yadda aka hana Muammar Gaddafi shigo da makamai Najeriya sau biyu karkashin mulkin Obasanjo, tare da rakiyar sojojinsa mata.
Gwamnatin tarayya ta amince kamfanonin sadarwa su yi ƙarin kudin kiran waya, sako da sayen data amma ba zai kai kaso 100% ba in ji ministan sadarwa, Bosun Tijani.
Ministan sadarwa na Najeriya, Bosun Tijani ya shiga taro da wakilan kamfanonin sadarwa da ke aiki a kasar nan kan bukatarsu na kara kudin kira da data.
Shugaban kamfanin mai na ƙasa NNPCL, Malam Mele Kyari ya bayyana yadda ya sha fama da kalubale a rayuwarsa tun daga almajiranci har matsayin da ya taka.
Shugaban kwamitin gyaran haraji na shugaban kasa, Taiwo Oyedele ya ƙara bayani kan kudirin harajin da ake ta cece kuce a jansa, ya ce Legas za ta fi asara.
Farfesa Banji Akintoye ya ce Yarbawa miliyan 60 suna goyon bayan neman ƙasar Yarbawa cikin lumana, bisa hakkin cin gashin kai na dokar Majalisar Dinkin Duniya.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari