Hukumar EFCC
Hukumomin EFCC da DSS sun fito sun yi magana kan zarge-zargen da ke cewa sun tilastawa shugaban kamfanin man fetur na kasa, Bayo Ojulari yin murabus daga mukaminsa.
Majiyar gwamnati ta karyata jita-jitar cewa Ojulari ya yi murabus daga shugabancin NNPCL kan badalar $21m. Ana zargin wasu kungiyoyi da yi masa bita-da-kulli.
Masu damfara na amfani da ₦500 a matsayin gudunmawar karya don satar bayanan sirrin jama'a da safarar kudi ta hanyar bude asusu a bankunan intanet.
EFCC ta kama Hamisu Breaker da G-Fresh kan likin Naira a wajen biki, inda kotu ta yanke musu hukuncin daurin watanni 5 ko biyan tarar N200,000 kowannensu.
Kungiyar AEISCID ta bukaci gwamnan Ebonyi ya kori sakatariyar gwamnatin jihar, Farfesa Umezuruike bayan kotu ta kwace N1bn da ake zargin na sata ne.
Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ta'annati da dukiyar kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya bayyana cewa ana bincikar wasu gwamnoni a Najeriya.
Babbar kotun tarayya da ke Maitama Abuja, ta yi hukunci kan bujatar da.tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya gabatar a gabanta ta neman a sakar masa fasfo.
A labarin nan, za a ji cewa tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose ya yi nasara a kotu bayan ta wanke shi daga zargin hukumar yaki da cin hanci da rashawa.
Shugaba Goodluck Jonathan ya zargi Muhammadu Buhari da gallazawa jami'an gwamnatinsa kan zarginsu da hannu a badakalar Malabu da aka yi a shekarun baya.
Hukumar EFCC
Samu kari