Bello Turji
Gwamnatin Zamfara ta karyata ikirarin yan bindiga cewa sun kama kanin Gwamna Dauda Lawal, ta ce suna amfani da fursunoni wajen yaɗa ƙarya da ƙara wa kansu ƙarfi.
Wasu rahotanni da muke samu sun tabbatar da cewa Bello Turji yana neman a yi sulhu bayan mutuwar dan uwansa kuma kwamandansa, Kachalla Yellow Danbokolo a Zamfara.
Bayan Bello Turji ya gwabza da jami'an tsaro, gwamnatin Zamfara ta ce artabun da aka yi da ‘yan ta'adda ya zama gagarumar nasara wurin kisan yaran dan bindigar.
Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa dan bindiga, Bello Turji ya bukaci N50m daga mazauna Tsalaken Gulbi da ke karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara.
Yayin da ake fama da ta'addanci a Zamfara, shugabannin Fulani sun koka kan yadda ake nuna musu wariya da zalunci duk da cewa su ba duka ‘yan ta’adda ba ne.
Sojojin Najeriya sun hallaka babban abokin Bello Turji mai suna Shaudo Alku a jihar Sokoto. An kashe dan ta'addan tare da tarin mayaka suna shirin tattaunawa.
Barazanar Bello Turji ta tilasta mazauna Sokoto da Zamfara barin gidajensu yayin da hare-haren 'yan bindiga ke kara kamari a kauyuka daban-daban na jihohin.
Yan bindiga sun sake kai muggan hare-hare a wasu yankunan Sokoto inda aka yi ajalin mutane wanda ake zargin yaran Bello Turji da daukar nauyin harin.
Rahotanni da muke samu sun tabbatar da cewa ƴan bindiga da ake zargin yaran Bello Turji ne sun kai farmaki garuruwa da ke karamar hukumar Isa a Sokoto.
Bello Turji
Samu kari