Arewa
A labarin nan, za a ji cewa kungiyar bayar da agaji ta ICRC ta bayya fargaba kan halin yunwa da kananan yara da mata ke fuskanta a Arewa maso Gabas.
A Alkaleri, mahaifar gwamnan Bauchi, 'yan bindiga sun kashe mutum ɗaya yayin da suka yi garkuwa da mutane 26. An fara tura masu Naira miliyan 1.5 na kudin fansa.
NiMet ta yi hasashen ruwan sama hade da tsawa da iska a jihohin Arewa da Kudu; an shawarci jama’a su guji fakewa a ƙarƙashin bishiyoyi da kuma tuki cikin ruwa.
Tsohon gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom ya ce bai tsani Muhammadu Buhari ba kamar yadda ake zargi amma ya soki salon yaki da matsalar tsaro a jiharsa.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya canza sunan titin Shendam zuwa titin Muhammadu Buhari domin karrama marigayi tsohon shugaban ƙasar Najeriya.
Manoma sun fara ajiye noma masara da sauran abubuwand suke bukatar taki saboda tashin farashi. Ana fargabar hakan zai iya haifar da karancin abinci a Najeriya.
Ana zargin Dr. Olabode Ibikunle ya rasu a otal yayin lalata da ɗaliba a Kogi, bayan ya sha maganin ƙara kuzari, kuma yanzu ’yan sanda na ci gaba da bincike.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta caccaki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu kan rabon mukaman da ta yi a baya-bayan nan. Ta ce ba da zuciya daya aka yi ba.
Wasu daga cikin shugabannin da suka shugabanci Najeriya, sun rasu bayan sun bar mulki. Shugabannin sun rasu ne bayan sun bar fadar Aso Rock da ke Abuja.
Arewa
Samu kari