Majalisar dokokin tarayya
A yau Talata majalisar dokokin jihar Rivers mai goyon bayan Gwamna Siminalayi Fubara ta tsara tantance waɗanda za su maye gurbin kwamishinonin Nyesom Wike.
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta gwangwaje yan majalisar jihar da motocin kece raini guda 41. An sayi kowace Toyota Fortuner a kan ₦68m.
Manyan kamfanonin siminti irinsu Dangote, BUA da IBETO sun ki amsa kiran da majalisa ta musu domin sauke farashin siminti. Sun tafi kotu neman kariya.
Jama'ar yankin mazabar Kaura Namoda/Birnin Magaji karkashin Coalition for Sustainable Development sun koka kan dan Majalisa, Sani Jaji tare da shirin masa kiranye.
Wani ɗan rikici ya faru tsakanin jami'an hukumar ƴan sandan farin kaya DSS da wasu ma'aikata a zauren majalisar tarayya da ke Abuja, tuni dai an shawo kan lamarin.
Jam'iyyar APC reshen jihar Zamfara ta tabbatar da dakatar da mamba mai wakiltar Kaura Namoda da Birnin Magaji, Aminu Sani Jaji kan zargin cin amana.
Majalisar dattawa ta zartar da kudurin dokar kafa hukumar raya Arewa maso Yamma. Idan aka kafa hukumar, za ta inganta rayuwa da farfado da tattalin arzikin shiyyar.
An tafka muhawara a majalisar wakilai kan ko shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima za su rika amfani da jirgin haya maimakon na fadar gwamnati.
Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyana kujerar marigayi Hon. Isa Dogonyaro babu kowa bayan ya rasu a ranar Juma'a da ta gabata a birnin Abuja.
Majalisar dokokin tarayya
Samu kari