Yan ta'adda
'Yan ta'addan Boko Haram masu tayar da kayar baya sun dasa bam a jihar Borno. Fashewar bam din ta jawo an samu asarar rayukan mutane tare da raunata wasu da dama.
Yayin da ake ta maganganu kan matsalar tsaro, jigo a APC, Yerima Kareto, ya bukaci Ministan yada labarai, Mohammed Idris ya kai ziyara wuraren da Boko Haram ke iko.
Rahotanni sun bayyana yadda babban jigo a jam'iyyar APC, Rauf Adeniji ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane, bayan sace shi a watan Janairun shekarar 2025.
Tsohon Ministan wasanni a gwamnatin Muhammadu Buhari, Solomon Dalung ya bayyana cewa akwai babbar barazana a yadda 'yan ta'adda ke cin karensu babu babbaka.
Rundunar 'yan sanda ta ceto mutane 17 da aka sace a jihar Kaduna tare da kwato manyan bindigogi har 21 a cikin wata motar haya. Sun gwabza fada da yan fashi.
Wasu mazauna karamar hukumar Anka a jihar Zamfara sun yabawa Bola Tinubu da ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle kan kakkabe yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma
Gwamnatin jihar Yobe karkashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni ta bayyana cewa ta shirya shigar da tubabbun 'yan ta'addan Boko Haram cikin al'umma.
Wasu rahotanni sun ce hare-haren sojoji a Danjibga da wasu dazukan Kudancin Zamfara na tilasta wa 'yan bindigar guduwa daga maboyarsu a Zamfara zuwa Sokoto.
Ma'aikatar yada labaran Najeriya ta karyata labarin da ke cewa Ministanta, Mohammed Idris ya nemi a yi fatali da kalaman gwamnan jihar Borno kan rashin tsaro.
Yan ta'adda
Samu kari