Yan ta'adda
Rundunar sojin saman Najeriya ta tabbatar da halaka 'yan bindiga a dajikan kananan hukumomin Giwa da Igabi a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne cikin makon da ya gabata.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana harin kunar bakin wake da 'yan ta'adda suka kai a jihar a matsayin kokarin yiwa gwamnatinsa zagon kasa.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar kubutar da wasu mutum 57 da 'yan ta'addan Boko Haram suka sace a dajin Sambisa. Sojojin sun kuma hallaka 'yan ta'adda.
Wasu 'yan ta'adda sun balle gidan gyaran hali a kasar Nijar. Hakan yayi sanadin tserewar daruruwan mayakan ta'addancin Boko Haram da masu safarar kwayoyi.
Hedikwatar tsaro ta DHQ a jiya Alhamis ta ce sojoji sun dakile shirin da ‘yan ta’adda ke yi na lalata wasu muhimman kadarorin Najeriya. DHQ ta yi karin haske.
Gwamnatin jihar Borno ta samar da tsarin mayar da tubabbun 'yan ta'addan Boko Haram zuwa cikin al'umma. Ya zuwa yanzu ta mayar da mutum 8,940 da suka tuba.
Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar hallaka yan ta'adda a jihohin Anambara, Katsina da Oyo. Ta kwato tarin makamai da kama dan ta'addan da ake nema ruwa a jallo.
Bayan shafe kwanaki 15 a hannun masu garkuwa da mutane, yaran mai Shari'a Janet Galadima sun shaki iskar 'yanci. Yanzu haka yaran na tare da mahaifiyarsu.
Shugaban jami'ar Dutsin-ma a jihar Katsina (FUDMA), Farfesa Armaya'u Bichi ya zargi wasu ma'aikatan jami'ar da aiki da 'yan ta'adda ta hanyar ba su bayanai.
Yan ta'adda
Samu kari