Magidanci Mai Mata 4 Da 'Yaya 34 Sun yi Rijistan Zabe, Yace Atiku Duk Zasu Kadawa Kuri'u

Magidanci Mai Mata 4 Da 'Yaya 34 Sun yi Rijistan Zabe, Yace Atiku Duk Zasu Kadawa Kuri'u

  • Wani Manomi ya saki hotunan iyalinsa kuma yayi alkawarin Alhaji Atiku Abubakar zasu zaba
  • Atiku Abubakar, shine dan takaran kujeran shugaban kasa karkashin jam'iyyar adawa ta PDP
  • Hukumar INEC ta shirya gudanar da zaben shugaban kasa a watan Febrairu, 2023 idan Allah ya kaimu

Wani Magidanci mai mata hudu da 'yaya 34 ya saki hotunan iyalansa da sukayi katin rijistan zabe kuma ya bayyana mutum 1 da dukkansu zasu kadawa kuri'a a zaben 2023.

Magidancin wanda Manomi ne mai suna Yusuf Babale yana da shekaru 49 a duniya.

Ya bayyana cewa da shi, da matansa hudu, da 'yayansa 34 dukkan dan takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP, Atiku Abubakar, zasu kadawa kuri'a a zaben 2023.

A hoton da wani Isreal Bulus ya dora a manhajar Facebook, an ga 'yayan mutumin maza da mata rike da katunan zabensu.

Kara karanta wannan

Daga karshe Atiku Abubakar ya yi maganar ‘rigimarsa’ da Gwamna Wike a PDP

Babale ya bayyana cewa Atiku Abubakar kadai ne wanda zai iya hada kan kasar nan duk halin rashin tsaro da wahala da ake ciki.

Kalli hotunansu:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Yaya 34
Magidanci Mai Mata 4 Da 'Yaya 34 Sun yi Rijistan Zabe, Yace Atiku Duk Zasu Kadawa Kuri'u Hotuna: Isreal Bulus
Asali: Facebook

Mai 4
Magidanci Mai Mata 4 Da 'Yaya 34 Sun yi Rijistan Zabe, Yace Atiku Duk Zasu Kadawa Kuri'u Hotuna: Isreal Bulus
Asali: Facebook

Daga karshe Atiku Abubakar ya yi maganar ‘rigimarsa’ da Gwamna Wike a PDP

Atiku Abubakar mai neman zama shugaban Najeriya a karkashin PDP ya gargadi jagororin jam’iyyar hamayyar game da sakin bakinsu.

The Cable ta kawo rahoto a daren Juma’a, 26 ga watan Agusta 2022 cewa Atiku Abubakar ya bukaci manyan PDP su guji kalaman da za su raba kai.

Ganin yadda wasu ke sakin kalamai a game da abubuwan da ke faruwa a jam’iyya, ga kuma zabe ya karaso, Atiku ya fadawa abokan aikinsa su yi hattara.

A wani jawabi da ya fito daga bakin Paul Ibe, ‘dan takaran shugaban kasar ya nuna cewa babu rabuwar kai tsakaninsa da ‘yan bangaren Nyesom Wike.

Asali: Legit.ng

Online view pixel