Matashin da zai yi takarar Shugaban kasa a APC, ya nemi ayi masa karo-karon kudin fam
- Adamu Garba ya nuna da gaske yake yi wajen neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki
- Duk da jam’iyyar ta tsawwala kudin fam, Malam Adamu Garba II sam bai da niyyar hakura da burin na sa
- Matashin ‘dan siyasar ya fito Facebook da Twitter ya bada lambobin akawun domin karbar gudumuwa
Malam Adamu Garba II ya fara yakin neman zaben shugaban kasa gadan-gadan, ya yi kira ga mutane su taimakawa wannan tafiya da ya dauko.
Legit.ng Hausa ta fahimci Adamu Garba II ya saki lambobin akawun na banki ga masoyansa domin a taimaka masa da kudin da zai yanki fam a APC.
Garba ya ce duk da fam din takarar shugaban kasa a APC ya yi tsada, ba zai karaya da yin takara ba, domin ya nuna cewa irinsa sun damu da kasar nan.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/ee0b8373124beb29.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
N50m na ware tun farko, Minista ya fadi hanyar da zai tara N100m na sayen fam a APC
Bayan ya rubuta sakon bara a Facebook, Garba II ya rubuta irin makamancin wannan a Twitter.
“Ya ku mutanen Najeriya. Na soma wannan tafiyar. Ga wadanda suka yi alkawarin bada gudumuwa, ga lambar akawun nan.”
“1008404148 | Bankin Zenith. Ba a duba kafin a tsaida kudin fam a N100m ba.”
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
“Amma hadin-kan da za mu yi wajen bada gudumuwar nan zai nuna da gaske mu ke yi, mun damu da halin da Najeriya ke ciki.”
![Adamu Garba Adamu Garba](https://cdn.legit.ng/images/1120/683e4b31ab7c5625.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
“Mu na bada shawarar ku hada da lambarku wajen turo kudin, ko kuma kira wadannan lambobin:
09034766771
08133068988
08060183701
Za kuma ku iya kiran wadannan lambobi da ke sama domin ka bada gudumuwarku.
Nagode.”
Martanin mutane a Facebook
Irinsu Abdussalam Muhammad Kazeem sun ce Allah dai ya bada sa’a, amma ba da su ba. Shi kuma Abdussalam Abdullahi ya ce tamkar a ba APC kyauta ne.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/6866172972da508e.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Kin jinin Musulmi: China ta yi Allah wadai da wadanda suka kona al-Qur'ani a Sweden
Wallahi gara kuɗin su zube ɓarawo ya tsinta.
- Sada Suleiman Usman
Akalla kafin ka bada lambar akawun, sai ka fada mana nawa ka ke da shi tukuna a kasa.
- Husaina Sufyan Ahmed
Ka fara bara ne. Idan ka samu, wa zaici Kudin? Hauka akeyi aka ce maka.
- Najeeb Nobel
Baba Buhari ya Sha mu, mun warke. Idan mun hada maka Kudin form yaya zaka Yi da delegates?
- Sani Labaran
Za mu bada gudumuwa
Allah Ya Tabbatar Da Alkhairi. Za Mu Yada; Za Mu Saka - Insha'Allahu.
- Muhammad Bashir
Allah Ya Tabbatar Da Alkhairi. Za Mu Yada; Za Mu Saka - Insha'Allahu.
- Abdullateef Hamza
Asali: Legit.ng