Ana tare: El-Rufai, Ganduje da Gwamnoni 6 da suka taba mika mulki ga Mataimakansu
- Gwamna Darius Ishaku ya taba shafe kimanin watanni uku ba ya Taraba. Amma duk tsawon wannan lokaci bai mika mulki ga mataimakinsa ba
- Amma akwai wasu gwamnoni da suke yin akasin abin da Gwamna Darius Ishaku ya yi, su kan bada rikon mulki na rikon kwarya idan har ba su gari
- Haka ta faru da gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu lokacin da ya kamu da cutar COVID-19 a 2021, ya ki ba Agboola Ajayi daman rike gwamnati
Abin da doka ta ce shi ne Gwamna ya mika mulki ga mataimakinsa idan ba ya ofis. Gwamnan zai yi hakan ne ta hanyar aika takarda ga majalisar dokoki
A wannan rahoto, Legit.ng ta kawo jerin Gwamnonin da suka taba mikawa mataimakansu mulki:

Kara karanta wannan
Babu wani amfani: Masari ya nemi a bude iyakokin Katsina yadda aka bude na sauran Jihohi
1. Nasir El-Rufai
Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya saba barin jihar Kaduna a hannun mataimakansa. An yi haka a lokacin Barnabas Yusuf Bala yana mataimakinsa.
Musamman lokacin da yake karatun PhD a kasar waje, Malam El-Rufai yana bada aron mulki, har an taba yin lokacin da Hon. Aminu Shagali ya ke rike da jihar.
A 2020 Mai girma Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa bar mataimakinsa ya zama gwamnan rikon kwarya a lokacin da ya je ganin likita a Amurka.
Gwamna Sule ya sanar da majalisar jiha game da tafiyarsa, ya bar mataimakinsa ya rike jihar.

Source: UGC
3. Babagana Umara Zulum
An yi lokacin da Usman Kadafur ne yake jan ragamar gwamnatin jihar Borno, a lokacin da Mai girma Farfesa Babagana Umara Zulum ya je hutun kwana 21.

Kara karanta wannan
Gyadar doguwa: Gwamna ya canza rayuwar 'yan mata 2 daga haduwa da su a hanyar kauye
Kafin ya je hutun, Gwamna Babagana Umara Zulum ya aikawa majalisar dokokin Borno takarda.
Kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada, gwamnan Rotimi Akeredolu ya kyale Lucky Orimisan Aiyedatiwa ya zama gwamnan rikon kwarya a 2021.
Akasin abin da ya faru da yake rigima da Agboola Ajayi, Akeredolu yana ba Aiyedatiwa dama.
5. Okezie Ikpeazu
A watan Yunin 2020, Mai girma gwamna Okezie Ikpeazu na jihar Abia ya sanar da Duniya cewa ya kamu da cutar COVID-19, hakan ta sa ya killace kan shi a gida.
Okezie Ikpeazu ya bar mataimakin Gwamnan jihar Abia, Rt Hon Ude Oko Chukwu ya zama gwamnan rikon kwarya a lokacin da yake jinya kafin ya samu lafiya.
6. Abdullahi Umar Ganduje
A Disamban shekarar bara Nasir Gawuna ya zama gwamnan rikon kwarya a jihar Kano. Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya mika masa ragamar mulki da ya bar kasar.
Gwamna Ganduje ya bar jihar a hannun Nasiru Gawana da ya je yin kwas a jami’ar Harvard da ke kasar Amurka. Ba wannan ne karon farko da Ganduje ya mika mulki ba.

Kara karanta wannan
Sabon lale: Atiku ya jefar da abokin takararsa, zai zabi Gwamnan PDP ya yi masa mataimaki
Asali: Legit.ng