Karya ake yi mani na cewa ina shirin barin PDP, in sake komawa APC inji Rabiu Kwankwaso

Karya ake yi mani na cewa ina shirin barin PDP, in sake komawa APC inji Rabiu Kwankwaso

  • Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya musanta raɗe-raɗin komawa jam’iyyar APC
  • Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da Channels TV a ranar Lahadi
  • Kwankwaso ya tabo batun kiran da ake yi na cewa ya kama kujerar shugaban kasa ya bar Arewa a 2023

FCT, Abuja - An yi hira da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso a game da batun da yake ta yawo na komawarsa jam’iyyar APC mai mulki.

A wata tattaunawa da ya yi da gidan talabijin na Channels TV, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso yace babu gaskiya a wannan jita-jita da yake ta yawo a yau.

A cewar Kwankwaso wanda ya yi gwamna a Kano, labarin karya ne kurum wasu suka kitsa. BBC ta fitar da wannan rahoto a ranar 9 ga watan Junairu, 2022.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Ministan Buhari ya bayyana yarjejeniyar da aka yi tun wajen kafa APC

Babban ‘dan siyasar yake cewa ya na murna da jin yadda wasu daga cikin mutanen da ya yi aiki da su a APC suke ta yada labarin dawowa jam’iyyar ta su.

“Ina farin cikin yadda mu ke ciki, mu na bakin kokarinmu a jam’iyyar PDP wajen ganin an samu nasara. Nan da karshen shekara, komai zai fito fili sosai”
“Siyasa na sauyawa, a da mu na APC, sai mu ka dawo PDP. Mu na cikin wadanda aka kafa jam’iyyar PDP da su a 1998, har na yi dacen zama gwamna.”

- Rabiu Kwankwaso

Rabiu Kwankwaso
Gwamna Ganduje da Rabiu Kwankwaso Hoto: Kwankwasiyya
Asali: Facebook

PDP tayi mani alheri

“A jam’iyyar PDP ne na zama gwamna a 1999, kuma na zama Ministan tsaro na kasa. Haka zalika a gwamnatinta ne nayi aiki a hukumar NDDC ta tarayya.”

Kara karanta wannan

Takarar shugaban kasa a 2023: Kwankwaso ya magantu kan yiyuwar tsayawarsa takara

Mulki ya koma kudu?

“Mutane su na cakuda abin da bai kamata a cakuda ba. Mu na da jam’iyyu dabam-dabam, inda kowace jam’iyya za ta kai takara, ya ragewa dabararta.”
"Idan aka duba zuwa 2023, jam’iyyar APC tayi mulkin shekara takwas, PDP kuma tayi 16. A cikin 16 da PDP tayi, Kudu tayi shekara 14, Arewa tayi biyu."

A dalilin haka, Kwankwaso yace ya ragewa kowace jam’iyya ta duba ta ga abin da za tayi domin ta kashe zabe, ba wai a tursasawa kowa inda zai kai takara ba.

Abiola, Obasanjo, Jonathan

A wannan hira da Seun Okinbaloye, Kwankwaso ya bayyana yadda ya rika marawa ‘yan takarar shugaban kasan da suka fito daga yankin kudancin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel