Komai ya na iya faruwa a 2023 – Kwankwaso ya tanka masu rade-radin sake shiga APC

Komai ya na iya faruwa a 2023 – Kwankwaso ya tanka masu rade-radin sake shiga APC

Rade-radi su na ta yawo a game da sauya-shekar Rabiu Musa Kwankwaso daga PDP zuwa jam’iyyar APC

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya amsa wannan tambaya da kan sa a wata doguwar hira da ya yi kwanan nan

Punch ta tambaye shi ko da gaske ya na shirin shiga APC idan an karbe ta daga hannun Abdullahi Ganduje

Abuja - Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyanawa Punch cewa a harkar siyasa komai ya na iya faruwa, ya kuma bayyana akidarsa da irin burinsa.

Hadimin 'dan siyasar, Saifullahi Muhammad Hassan ya tsakuro wannan hira a shafinsa na Facebook.

“A siyasa komai mai iya yiwuwa ne. Ba mu bukatar makiya na din-din-din, abin da muke so shi ne masoya na din-din-din, wannan na da muhimmanci.”

Kara karanta wannan

Yadda ɗan gani kashenin Buhari ya koma Kwankwasiyya bayan ƴan bindiga sun sace ƴan uwansa 5

“Masoya mu ke nema, zai ba ka sha’awa cewa a cikin wadanda muka fara siyasa da su shekaru 30 da suka wuce, wasu su na raye, kuma mu na nan tare.”

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Har ma wadanda suka rasu shekaru 30 da suka wuce zuwa yanzu su na cikin ranmu, shekara- shekara mu kan samu danginsu, mu yi masu wani abu.”
“Saboda haka a zaben 2023, na yi imani cewa abubuwa da yawa za su iya faruwa.” – Kwankwaso.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso
Tsohon shugaban PDP, Saraki da Kwankwaso kafin zaben 2019 Hoto: @SaifullahiHon
Asali: Twitter

Sai yadda kotun koli tayi da PDP

A game da komawa jam’iyyar APC da ya bari a 2018, tsohon Sanatan na Kano ta tsakiya yace a halin yanzu makomar jam’iyyar PDP ta na ga kotun koli.

“PDP ta shirya zaben shugabanninta, shakka-babu tsohon shugaban jam’iyya na kasa, Uche Secondus ya na kotu, kuma kotun koli za ta yi hukunci.”

Kara karanta wannan

Ina goyon bayan Buhari kan kin sanya hannu a dokar zabe, Sanata Adamu

“Hukuncin da kotun koli za tayi kwanan nan zai yi tasiri a kan makomar jam’iyyar (PDP). Haka zalika matakin da shugabannin jam’iyya suka zartar.”

- Kwankwaso

Kwankwaso wanda yayi gwamna sau biyu a Kano yace jam’iyya ta na iya biyewa gwamnoninta 13, tayi watsi da maganar duk sauran ‘ya ‘ya da magoyanta.

A gefe guda kuma, ‘dan siyasar ya bada shawarar cewa a ajiye girman kai, a tafi da kowa, yace wannan shi ne zai taimakawa jam’iyyun siyasa a wajen zabe.

A cewar Kwankwaso, ita ma APC ta na yin irin na ta shirin wanda idan tayi kuskure za ta auka cikin rigimar da ta fi ta PDP, yace burinsa a samu shugaba na gari.

Mu na lale da Kwankwaso - Babafemi Ojudu

A jiya ne aka ji Hadimin shugaban kasa, Babafemi Ojudu yace zuwan Kwankwaso APC zai amfane su domin shi gawurtaccen ‘dan siyasa ne mai jama’a tare da shi.

Kara karanta wannan

Abin da ya sa matsalar tsaro ke neman gagarar hukuma - Hamza Al-Mustapha ya fadi sirrin

A gefe guda, Mai magana da yawun bakin tafiyar Kwankwasiyya, Sunusi Bature Dawakin Tofa yace jita-jitar sauya-shekan duk ba su da asali ko tushen kamawa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel