Mama Taraba, Mantu, tsofaffin Gwamnoni, Ministoci, ‘Yan Majalisa 25 da aka rasa a 2021
- A shekarar nan ta 2021 da ake shirin fita, an samu mace-macen manyan mutane da-dama a Najeriya.
- Legit.ng Hausa ta tattaro jerin wasu ‘yan siyasa da masu mulki da suka rasa ransu a shekarar nan
- Daga cikinsu akwai matan tsofaffin shugabannin kasa, Shehu Shagari da kuma Janar Aguiyi-Ironsi
Tsofaffin Ministocin da suka rasu a shekarar nan sun hada da wadanda suka rike mukamai a mulki soja na farar hula irinsu tsohon Jakada, Bunu Sheriff.
Daga cikin tsofaffin Ministoci akwai
1. Tony Anenih (Tsohon Ministan wasanni)
2. Bunu Sheriff
3. Mahmud Tukur
4. Hussaini Zanwa
5. Abba Sayyadi Ruma
6. Malami Buwai
7. Bala Ka'oje (Tsohon Ministan matasa da wasanni da Sanata)
8. Dr. Halliru Alhassan (Tsohon Ministan kiwon lafiya)
Irinsu Sanata Jummai Alhassan, Cif Tony Momoh da Lateef Jakande sun rike mukamai da-dama baya ga Minista da suka yi. Akwai gwamnonin soji 3 da suka rasu.
Tsofaffin gwamnonin soja da farar hula
9. Lateef Jakande (Tsohon Gwamnan Legas, tsohon Ministan Abacha)
10. Dominic Oneya (Tsohon Gwamnan soja Kano, tsohon shugaban NFA)
11. Anthony Ukpo (Tsohon Gwamnan soja na Ribas)
12. Adetunji Idowu Olurin (Tsohon Gwamnan soja na Oyo)
Tsofaffin ‘Yan majalisar tarayya:
13. Joseph Wayas (Tsohon shugaban majalisar dattawa)
14. Ibrahim Nasiru Mantu (Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa)
15. Biyi Durojaiye (Tsohon Sanatan Legas)
16. Hosea Ehinlanwo (Tsohon Sanatan Ondo)
17. Gbenga Aluko (Tsohon Sanatan Ekiti)
18. Nuhu Aliyu (Tsohon Sanatan Neja)
19. Sati Gogwim (Tsohon Sanatan Filato)
20. Haruna Maitala (Tsohon ‘dan majalisar tarayya)
Sauran manyan ‘yan siyasa na kasa:
21. Dr. Adegbola Dominic (Shugaban PDP na jihar Legas)
22. Dr. Obadiah Mailafia (Tsohon gwamnan CBN)
Matan manyan kasa:
23. Hadiza Shehu Shagari
24. Victoria Jonathan Aguiyi-Ironsiga
Na karshe a jerin na mu, wani dattijo ne wanda ya rike mukamai da-dama a gwamnatin tarayya:
25. Ahmad Joda
Asali: Legit.ng