Zaben Anambra: Mala Buni, Peter Obi, Uzodinma da manyan mutane 4 da APGA ta tonawa asiri

Zaben Anambra: Mala Buni, Peter Obi, Uzodinma da manyan mutane 4 da APGA ta tonawa asiri

  • Jam’iyyar APGA ta sake lashe zaben jihar Anambra, za ta cigaba da mulkar jihar har nan da 2025.
  • Baya ga ‘Yan takara 18 da Charles Soludo ya doke, akwai ‘yan siyasan da suka ji kunya a zaben.
  • Abin da ya kara ba mutane mamaki shi ne yadda Soludo ya doke Ozigbo har a kauyen Peter Obi.

Anambra - Jam’iyyar All Progressive Grand Alliance watau APGA ce tayi nasara a zaben sabon gwamnan jihar Anambra, ta doke jam’iyyu har 18.

Jaridar Daily Trust ta kawo jerin wasu ‘yan siyasa da suka sha kashi a zaben. Wadannan mutane su ne nasarar Chukwuma Soludo za ta fi yi wa ciwo.

1. Nkem Okeke

Nkem Okeke shi ne mataimakin gwamna Willie Obiano a karkashin APGA. Daf da zabe ya sauya-sheka zuwa APC, amma bai iya tsinana mata komai ba.

Kara karanta wannan

Zaben Anambra: Dalilai 5 da suka sa PDP ta sha mummunan kaye a zaben gwamna

2. Peter Obi

An yi mamakin yadda Peter Obi wanda ya yi takarar mataimakin shugaban kasa a PDP a 2019 ya gaza tabuka wani abu a zaben duk da ya yi gwamnan jihar.

3. Mai Mala Buni

Zaben Anambra bai yi wa shugaban rikon kwarya na APC, Mai Mala Buni dadi ba. Buni ya sa ran APC za ta karbe Anambra kamar yadda ta fara mamaye yankin.

Zaben Anambra
Sanata Andy Uba Hoto: www.sunnewsonline.com
Asali: UGC

4. Hope Uzodinma

Za a ga laifin gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma a rashin nasarar Andy Uba. Uzodinma shi ne kusan jagoran jam’iyyar APC a yankin na kudu maso gabas.

5. Bianca Ojukwu

Bianca Ojukwu wanda ta yi Chukwuemeka Odumegwu takaba ta ji kunya a wannan zabe. Bianca ta samu sabani da jagororin APGA gabanin zaben gwamnan.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Daga ƙarshe, INEC ta ayyana wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Anambra

6. Stella Oduah

Wata mace da Daily Trust ta kawo a jerin na ta ita ce Sanata Stella Oduah wanda ta sauya-sheka zuwa APC. Uba ya sa rai tsohuwar Ministar ta taimaka masa.

7. Chukwuma Umeoji

Honarabul Chukwuma Umeoji mai wakiltar mazabar Aguata a majalisar wakilai ya ji kunya a zaben bayan rikicin tikiti da ya yi tayi da Charles Soludo a kotu.

Fadan Buhari da Ahmad Gumi

Ashe tun bayan zaben 2007, shugaban kasa Muhammadu Buhari yake rike Ahmad Gumi a rai, saboda ya bada shawarar ka da a shigar da Umaru 'Yar'adua kotu.

Tukur Mamu yace Gumi ya kara batawa Buhari rai a 2015, lokacin da ya bada shawarar shi da Goodluck Jonathan duk su hakura da shiga zaben shugaban kasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel