Ramadan: Zakir Naik Ya Jero Abubuwa 25 da za Su Sa Mai Azumi Samun Lada Mai Yawa
- Fitaccen Malamin Musulunci na duniya, Dr Zakir Naik ya yi wa al'ummar Musulmi nasiha game da ayyukan alheri da ya kamata su yi a Ramadan
- A nasihar da ya yi wa jama'a, Sheikh Zakir Naik ya lissafa muhimman abubuwa da suka hada da salloli, neman daren Lailatul Qadri da sauransu
- Hakan na zuwa ne yayin da al'ummar Musulmi a Najeriya da kasashe dadaban daban suka shiga kwana na 4 a watan Ramadan a fadin duniya
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - Malamin addinin Musulunci na duniya, Dr Zakir Naik ya bukaci Musulmai su dage da ibada yayin da watan Ramadan ke cigaba da tafiya.
Baya ga lissafa abubuwa 25 da ya kamata a mayar da hankali game da su a Ramadan, Sheikh Zakir Naik ya gargadi mutane kan kame harshe a Ramadan.

Source: Getty Images
Legit Hausa ta gano cewa malamin ya yi nasihar ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar 4 ga Ramadan 2026.
Kiran Zakir Naik kan abubuwa 25
Abubuwa 25 da Dr Zakir Naik ya bukaci Musulmi su yi a Ramadan sun hada da dagewa da salloli, yin sahur da sauransu. Ga jerin abubuwan a kasa:
1. Yin sallolin farilla guda biyar a cikin jam’i
2. Yin azumi a kowace rana ta Ramadan
3. Bayar da zakka idan ta wajaba a kan mutum
4. Nisantar dukkan abubuwan haram
5. Yin sallolin nafila, musamman kafin farillai da bayan su
6. Yin sahur
7. Jinkirta sahur zuwa kusa da asuba
8. Gaggauta buɗa baki
9. Cin dabino da shan ruwa yayin buɗa baki
10. Karanta addu’ar da ake yi bayan buɗa baki
11. Yin addu’a kafin buda baki
12. Ciyar da talakawa abinci
13. Yin sallar Tarawihi
14. Yin sallar walaha (aƙalla raka’a 4)
15. Yin sadaka da kyauta da yawa
16. Karanta addu’o’i masu yawa da suka shafi ayyukan yau da kullum
17. Yawaita ambaton Allah SWT (yin zikiri)
18. Karanta Alƙur’ani gwargwadon iko tare da fahimtar ma’anarsa
19. Neman gafarar Allah
20. Yawaita aikata ayyukan alheri
21. Idan wani ya tsokane ka, kada ka yi martani, sai ka ce “Ina azumi”
22. Yin i’tikafi a kwanaki 10 na ƙarshen Ramadan
23. Neman daren Lailatul Qadir
24. Yin sallar dare, musamman a kwanaki 10 na ƙarshe
25. Tsarkake zuciya
Malamin ya kara da cewa yana da kyau Musulmi ya sani cewa azumi ba ya inganta sai an nisanci ƙarya, alfasha da sauransu.
Bola Tinubu zai ciyar da talakawa
A wani labarin, kun ji cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa kwamitin ciyar da talakawa a watan Ramadan a fadin Najeriya.
Shugaban kasar ya nada Sarkin Kano na 15, mai martaba Aminu Ado Bayero shugabancin kwamitin domin lura da yadda zai yi aiki.
Kwamitin ya hada da malaman addinin Musulunci, ma'aikatan gwamnati da 'yan siyasa ciki har da Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

