Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano

Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano

  • Wasu mambobin jam'iyyar NNPP sun tafi zanga-zanga hedkwatar hukumar zabe ta INEC
  • Wannan ya biyo bayan zanga-zangan da suka yi jiya Talata kan kwamishanan da suke zargin za'a turo Kano
  • Yau dai saura kwanaki uku zaben gwamnonin Najeriya kuma ta jihar Kano na cikin masu zafi

Kano -Mambobin jam'iyyar adawa ta New Nigeria Peoples Party, NNPP, a jihar Kano sun fito zanga-zanga kan zargin cewa Sakataren hukumar zabe INEC na jiha ya hada kai da jam'iyyar APC.

Wannan sakatare na hukumar INEC da ake zanga-zanga a kansa sunansa Alh. Garba Lawan Muhammad.

Freedom Radio ta ruwaito cewa masu zanga-zangar na zargin Alhaji Lawan ya hada kai da jam'iyyar APC dake kan mulki don yin magudi a zaben gwamnan jihar.

An yi zanga-zanga ne gaban hedkwatar hukumar INEC dake Kano.

Kara karanta wannan

Muna Jiran Hukuncin Kotun ƙoli Akan Lamarin Shekarau Inji NNPP

Zaben gwamnan jihar Kano da sauran gwamnonin Najeriya zai gudana ne ranar 11 ga Maris, 2023.

Kalli hotunan:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Garba
Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano
Asali: Facebook

Garba
Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano
Asali: Facebook

Garba
Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano
Asali: Facebook

Garba
Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano
Asali: Facebook

Garba
Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sakataren INEC Dake Kano
Asali: Facebook

Mambobin Jam'iyyar NNPP Sun Fito Zanga-Zanga Kan Sabon Kwamishanan Yan Sandan Da Za'a Tura Kano

Jiya mun kawo muku labarin cewa mambobin jam'iyyar adawa ta New Nigeria Peoples Party, NNPP, a jihar Kano sun fito zanga-zanga kan zargin cewa hukumar yan sanda na shirin tura wani sabon kwamishanan yan sanda Kano.

Wannan kwamishana mai suna, Balarabe Sule, da NNPP ke zanga-zanga kansa, tsohon dogarin gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ne.

Tsohon Sakataren hukumar TetFund, Baffa Bichi, ne ke jagorantar wannan zanga-zanga.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel