Malami Dan Najeriya, Sheikh Adam Al-Fulany Ya Lashe Gasar Adabin Larabci a Maroko

Malami Dan Najeriya, Sheikh Adam Al-Fulany Ya Lashe Gasar Adabin Larabci a Maroko

  • Sheikh Adam Abdurrrahman Al-Fulany, Malamin Adabin Larabci Dan Najeriya Ya lashe gasar Larabci a kasar Maroko
  • Mutane sun yi mamakin yadda dan Najeriya ya kada Larabawa wajen gasar Uyoon El-Adab El-Arabi
  • Za'a gudanar da taron karrama Malamin wanda mazaunin jihar Kano ne a kasar Magrib a Nuwamba

Malamin Dan Najeriya kuma mazauni jihar Kano, Adam Abdurrahman Al-Fulany, ya zama gwarzon ilmin adabin larabci na shekarar 2022 na Uyoon El-Adab El-Arabi dake Kasar Maroko.

An karrama Malamin bisa ayyukan rubuce-rubucen da yayi wanda ya shafi adabi, tarihi, al'ada dss.

Za'a baiwa Al-Fulany kyauta na nasarar da ya samu a taron Uyoon El-Adab El-Arabi da za'ayi ranar 1 ga Nuwamba, 2022 a birnin Uyoon, Maroko.

Alfulany
Malami Dan Najeriya, Sheikh Adam Al-Fulany Ya Lashe Gasar Adabin Larabci a Maroko
Asali: Original

Wane ne Al-Fulany?

Malamin a 2021 ya lashe kasar adabin larabci na Hamsa dake Kahira, babbar birnin kasar Masar.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Kakakin Majalisar Dokokin Wata Jiha a Najeriya Ya Rasu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Cibiyar nazarin yaren Larabci ta Najeriya ce ta zabeshi don a bashi wannan kyauta.

An haifeshi ranar 30 ga Junairu, 1963, inda ya halarci makrantar Sakandaren Darul Ulum Ilori jihar Kwara da Markazul Duruusul Arabiyya dake Agege jihar Legas.

Ya samu digiri a ilmin adabin larabci daga jami'ar Bayero dake Kano a 1992 sannan ya yi Majistir a ABU Zaria a 1994.

Littafan da ya rubuta

Daga cikin littatafan da ya rubuta akwai:

Raai Al-Ganam

Ahl Al-Takror

‘Alat-Tariq

Jamiah Alarwah

Al-Gaibiyyat ala Dao’i Al-Ilm was Al-Deen

Muhimmah Al-Insan Ala Sath Al-Ard

Sira Al-Ajyal fi Qadaya Al-Islam

Hadithun maa Ulama Al-Hadith

Asali: Legit.ng

Online view pixel