Ziyarar Kaduna: Tinubu ya samu tabarraki daga wajen Sheikh Dahiru Bauchi

Ziyarar Kaduna: Tinubu ya samu tabarraki daga wajen Sheikh Dahiru Bauchi

  • Jigon jam'iyyar APC na kasa, Bola Tinubu, ya kai ziyara ga babban malamin Musulunci, Sheikh Dahiru Bauchi
  • Tinubu ya isa ga malamin ne a yayin da ya kai ziyarar jaje jihar Kaduna bayan harin jirgin kasa da ya faru a makon da ya gabata
  • Shehin malamin ya sakawa dan siyasar wanda ke neman shugabancin kasar albarka tare da yi masa tofin addu'o'i

Kaduna - Babban jagoran jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya ziyarci babban malamin addinin Musulunci, Sheikh Usman Dahiru Bauchi.

Tinubu wanda ke neman takarar shugabancin kasar a zaben 2023 karkashin inuwar APC, ya ziyarci Shehin Malamin ne a yayin ziyarar jaje da ya kai jihar Kaduna a ranar Talata, 5 ga watan Afrilu.

Ziyarar Kaduna: Tinubu ya samu tabarraki daga wajen Sheikh Dahiru Bauchi
Ziyarar Kaduna: Tinubu ya samu tabarraki daga wajen Sheikh Dahiru Bauchi Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

A daya daga cikin hotunan ziyarar tasa wanda tuni suka karade shafukan sadarwa, an gano Tinubu durkushe a gaban jigon na darikar Tijjaniyya yayin da shi kuma ya dafa kansa sannan ya saka masa albarka tare da yi masa tofin addu’o’i.

Kara karanta wannan

Najeriya na cikin wani hali: Tinubu ya ba wadanda harin 'yan bindiga na jirgin kasa ya shafa tallafin N50m

A wata wallafa da ya yi a shafinsa na Twitter wanda ke tabbatar da ziyarar da ya kaiwa Shehin Malamin, Tinubu yace sun tattauna lamura da dama.

Sai dai ya ce sun fi karkata ga yadda za a yi amfani da koyarwar addinin Islama wajen kawo karshen rikicin da kasar ke fama da shi musamman a wannan wata ta Ramadana.

Tinubu ya ce:

“Kafin na bar Kaduna, na kuma ziyarci mai girma Sheikh Dahiru Bauchi. Tattaunawarmu ta tabo batutuwa da dama amma ta karkata ga yadda za a iya amfani da koyarwar Musulunci wajen kawo karshen tashe-tashen hankula da rigingimu a kasar nan musamman a wannan wata mai alfarma.”

Najeriya na cikin wani hali: Tinubu ya ba wadanda harin 'yan bindiga na jirgin kasa ya shafa tallafin N50m

Kara karanta wannan

Ramadan: Bola Tinubu ya yi kira na musamman ga al’ummar Musulmi a kan watan azumi

A gefe guda, mun kawo cewa Bola Tinubu, ya koka kan yawan hare-haren ta’addanci da kasar ke fuskanta, inda ya ce Najeriya na zubar jini.

Tinubu wanda ya ziyarci jihar Kaduna domin yiwa gwamna Nasir El-Rufai jaje a ranar Talata, 5 ga watan Afrilu, ya ce akwai bukatar hada hannu domin yakar fashi da makamai da kuma ta’addanci.

Ya yi Allah-wadai da harin da yan bindiga suka kai kan jirgin kasar Kaduna a makon da ya gabata, inda ya bayyana lamarin a matsayin abun kunya, Daily Trust ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel