An tono badakalar Naira Biliyan 370 da aka tafka a kasafin kudin 2022 da Buhari ya sa hannu

An tono badakalar Naira Biliyan 370 da aka tafka a kasafin kudin 2022 da Buhari ya sa hannu

  • BudgIT ya yi ikirarin ya bankado badakalar da suke cikin kasafin kudin wannan shekarar ta 2022
  • An yi mai-men kwangiloli kusan 500 a kasafin bana, hakan za su jawo ayi awon gaba da N370bn
  • Binciken da aka yi ya nuna cewa ma’aikatun tarayya su na kakaba ayyukan bogi a kasafin kudinsu

Abuja - A ranar Litinin, 17 ga watan Junairu, 2022, BudgIT ta bayyana cewa ta gano an yi mai-men wasu ayyuka har 460 a kasafin kudin shekarar 2022.

BudgIT ta ce wadannan kwangiloli da aka maimaita a kundin kasafin kudin za su ci N378bn. Iyanu Fatoba ya bayyana wannan a wata sanarwa dazu.

Kamar yadda suka bayyana a shafinsu na Facebook, BudgIT sun ce akwai wasu kofofin satar dukiyar al’umma da aka bude a kundin kasafin kudin bana.

Kara karanta wannan

Ma’aikata sun fara salati, Gwamnatin Buhari za ta karbi aron N620bn daga asusun fansho

Daga ciki an ankarar da mutane cewa ma’aikatar muhalli ta ware N67.8m da sunan gina wuraren ajiye bindigogi a jihohi hudu, wanda wannan ba aikinta ba ne.

Kwangilolin bogi a Aso Rock?

Binciken da BudgIT ta yi, ya nuna cewa an kara kudin wasu kwangiloli na biliyoyi da za a yi a fadar shugaban kasa, daga ciki har da gini a asibitin Aso Villa.

Kasafin kudi
Kasafin kudin shekarar 2022 Hoto: www.channelstv.com
Asali: UGC

N20.7m aka ware da nufin gina sashen shugaban kasa a asibitin da ke cikin fadar Aso Villa, sai dai kuma a halin yanzu akwai wannan sashe a asibitin a gine.

Akwai N28.72m da aka sa a kundin kasafin kudin shekarar 2022 na sayen na’urorin sukola biyu da kuma talabijin na kirar LG a gidan gwamnati da ke Legas.

Babura za su ci N1.3bn a 2022

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: Wani mutum ya shiga hannu yayin da ya kashe yaransa uku ya adana gawarwakinsu a cikin firinji

National Agency for Great Green Wall da aka kafa domin magance matsalar cin kasa da samar da isasshen abinci za ta kashe N1.3bn a 2022 wajen sayen babura.

Shi ma wannan aiki na sayen babura da kafa fitulu a kan hanya da hukumar ta dauko ba ya cikin hurumin da aka ba ta a jihohi Arewacin Najeriya 11 da ta ke aiki.

A karshe BudgIT tayi kira ga gwamatin shugaba Muhammadu Buhari ta maida hankali wajen yin ayyukan da al’ummar kasar suke bukata a shekarar nan ta 2022.

Dokar zabe

A ranar Lahadin da ta wuce ne tsohon shugaban hukumar INEC, Farfesa Attahiru Jega ya bada shawarar a gyara dokar zabe na kasa kafin a shirya zaben 2023.

Farfesa Jega ya na ganin akwai wasu abubuwan alheri a kudirin zaben da shugaban kasa yi watsi da shi saboda wasu kura-kurai da aka samu tattare da shi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel