Jami’ar Masar da kasar UAE sun shiryawa mahaddata gasar karatun Kur’ani a Najeriya
- Jami’ar Al-Azhar Shereef ta Cairo ta shirya gasar karatun littafin Al-kur’ani a birnin tarayya Abuja
- Wakilan jami’ar da ke Masar sun gudanar da wannan musabaka ne da hadin-kan jakadancin kasar UAE
- Irinsu Ayman Esmat, Sheikh El-Hasanain El-Moallim da kuma Sheikh AbdelAzeem sun halarci gasar
Abuja - Kwararrun malamai daga jami’ar Al-Azhar Shereef da ke birnin Cairo, kasar Masar sun yi alkawarin cigaba da gudanar da musabaka a Najeriya.
Daily Trust ta fitar da rahoto a ranar Litinin, 13 ga watan Disamba, 2021, cewa jami’ar ta hada-kai da kasar UAE wajen shirya gasar Al-kur’ani a Abuja.
Wakilan jami’ar ta Al-Azhar Shereef sun bayyana wannan ne a ranar Lahadi, yayin da aka yi bikin rufe gasar da aka shirya na wannan shekarar.
An gudanar da wannan gasa ta karatun littafi mai tsarki a cibiyar raye karatun addinin musulunci da ke karkashin masallacin nan na An-Noor.
Manyan fuskoki a wajen gasar
Wadanda suka samu damar halartar musabakar su ne: Darektan Ustadh Abdallah Ahmad bangaren da’awa da yada ilmi na cibiyar addinin musuluncin.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Asali: UGC
Jaridar tace sakataren ofishin jakadancin Masar, Ayman Esmat wanda ya wakilci Jakadan kasar, Sheikh Zakariyya Al-azhari ya na cikin mahalartan gasar.
Imam Tamim Yusuf Alhasan, babban limamin masallacin Juma’a na Zone 3 ya zo wajen musabakar, haka zalika darektan ICICE, Kabir Kabo Usman.
Dalilin kiran irin wannan gasa
Dr. Kabir Kabo Usman a jawabinsa a madadin cibiyar masallacin An – Noor, ya yaba da kokarin da jami’ar take yi wajen bunkasa ilmin musulunci a Najeriya.
Sheikh Assayed El-Hasanain El-Moallim wanda ya shirya wannan musabaka, yace burinsu shi ne yada asalin manufar musulunci, su yaki tsattsauran ra’ayi.
Har ila yau, Sheikh Mahmood AbdelAzeem da yake magana, ya yi bayanin muhimmancin koyon Kur’ani. Za a cigaba da shirya irin wannan gasa a kai-a kai.
Aisha Yesufu ta yi magana
Aisha Yesufu ta fito ta na kokawa cewa a maimakon Jami’an tsaro su kare rayuka da dukuyoyin mutane, su na muzgunawa masu yin zanga-zanga a Arewa.
'Yar gwagwarmayar ta soki masu cewa a dage da addu'a, a guji yin fito na fito da shugabanni, tace hakan ba ya cikin koyarwar Manzon Allah (SAW) a musulunci.
Asali: Legit.ng