‘Yan bindiga sun yi wa ‘yan sanda kwanton bauna, sun yi awon gaba da bindiga

‘Yan bindiga sun yi wa ‘yan sanda kwanton bauna, sun yi awon gaba da bindiga

  • Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki tawagar 'yan sanda da ke sintiri a kan hanyar Kolo zuwa Ogbia a karamar hukumar Ogbia ta jihar Bayelsa
  • An tattaro cewa maharan da ake zaton 'yan kungiyar asiri ne sun harbi wani sufeton dan sanda sannan suka yi awon gaba da bindigarsa
  • Mai magana da yawun 'yan sanda a jihar Bayelsa, SP Asinim Butswat, ya tabbatar da afkuwar lamarin

Bayelsa - Wasu 'yan bindiga da ake zargin' yan kungiyar asiri ne sun kai hari kan tawagar 'yan sanda da ke sintiri a kan hanyar Kolo zuwa Ogbia a karamar hukumar Ogbia ta jihar Bayelsa.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa wani sifeton 'yan sanda ya samu rauni a harin yayin da aka kwace bindigarsa.

‘Yan bindiga sun yi wa ‘yan sanda kwanton bauna, sun yi awon gaba da bindiga
‘Yan bindiga sun yi wa ‘yan sanda kwanton bauna, sun yi awon gaba da bindiga Hoto: Premium Times
Asali: UGC

A cewar wata majiya daga yankin Kolo, lamarin ya faru ne mintuna kadan kafin tsakar dare a ranar Litinin.

Kara karanta wannan

Yanzu-yanzu: Yan bindiga sun kai hari ofishin yan sanda, sun saki wadanda aka tsare sun kona motocin sintiri

Ya ce a lokacin da mazauna garin suka ji harbin, sai suka yi tunanin 'yan bindiga ne ke kai hari garin.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kodayake akwai rahotannin da ba a tabbatar da su ba cewa an kashe wani Sufeto na 'yan sanda.

A ruwayar jaridar Sahara Reporters, ta tattaro cewa bayan ‘yan bindigar sun kashe wani jami’in dan sanda, sai suka yiwa ofishin ‘yan sandan na Kolo dalla-dalla sannan suka tafi da wasu harsasai.

Sai dai kuma, kakakin 'yan sanda a jihar Bayelsa, SP Asinim Butswat, ya ce Sufeton ya samu rauni ne kawai.

Butswat, yayin tabbatar da faruwar lamarin a kungiyar yada labarai WhatsApp na 'yan sandan jihar Bayelsa, ya ce ana ci gaba da bincike kan al’amarin.

Ya ce:

“Wasu ‘yan bindiga da ake zargin‘ yan kungiyar asiri ne, sun kai wa jami’an ‘yan sanda da ke gudanar da bincike a kan hanyar Kolo-Ogbia hari a ranar 11 ga Oktoba, 2021, da misalin karfe 22:45.

Kara karanta wannan

An kashe manoma uku a wani sabon hari da aka kai kan kauyen Filato

“Wani sifeton ‘yan sanda ya ji rauni sosai kuma an tafi da bindigarsa. Ana ci gaba da gudanar da bincike don cafke 'yan bindigar da kuma kwato bindigar da aka sace."

Ku ba 'yan bindiga hadin kai don tsira da rayukanku, shawarin 'yan sanda ga 'yan Najeriya

A wani labarin, Tribune Nigeria ta ruwaito cewa, a ranar Talatar da ta gabata ne Babbar Rundunar ‘Yan Sanda ta shawarci 'yan Najeriya da su ba da hadin kai ga masu garkuwa da mutane idan sun fada hannunsu don kare lafiyar su da kuma gujewa kashe su.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar (FPRO), Frank Mba, wani Kwamishinan 'yan sanda, ya ba da shawarar ne a Abuja yayin gabatar da mutane 48 da ake zargi da aikata manyan laifuka.

Wadanda ake zargin har da wani Haliru Mohammed mai shekaru 25 wanda ya shirya garkuwa da 'yar uwarsa, Binta, don ya karbi fansa saboda ya gaza biyanta bashin da ta ke binsa.

Kara karanta wannan

Zamfara: A kalla rayuka 12 sun salwanta, 'yan bindiga sun kone motar 'yan sanda

Asali: Legit.ng

Online view pixel