2023: Ghali Umar, Shehu Sani, Falana da wasu 'yan gwagwarmaya 27 sun kirkiro wani sabon salo na siyasa

2023: Ghali Umar, Shehu Sani, Falana da wasu 'yan gwagwarmaya 27 sun kirkiro wani sabon salo na siyasa

Yayin da babban zaben kasa na 2023 ke gabatowa, wasu mashahuran 'yan gwagwarmaya a Najeriya, malamai, da sauran kwararru 30, sun kirkiro wani sabon salo na siyasa wanda ake kira National Consultative Front.

Akidar wannan sabuwar tafiya ta siyasa, ba ta wuce hada kan 'yan Najeriya domin yi sauya fasalin kundin tsarin siyasa da kuma shimfidar wata sabuwar hanyar samar da sabon tsari na jagoranci.

Wannan yana ƙunshe cikin wata sanarwa da ta fitar bayan doguwar tattaunawa ta tsawon watanni da kuma taruka daban-daban da rika gudanarwa.

Kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito, wannan sanarwar ta fito ne a ranar Laraba daga babban ofishin kungiyar na kasa da ke birnin Abuja.

Ghali Na'abba, Oby Ezekwesili, Femi Falana da Shehu Sani
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Punch
Ghali Na'abba, Oby Ezekwesili, Femi Falana da Shehu Sani Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Punch
Asali: UGC

Daga cikin jerin kwamitin mutum 30 na 'yan gwagwarmayar da za su jagoranci wannan sabuwar tafiya ta siyasa, sun hadar da tsohon kakakin majalisar wakilai; Ghali Na'abba, tsohon mataimakin babban bankin Najeriya; Dr. Obadiah Mailafia.

Sauran sun hadar da; Olisa Agbkoba, Femi Falana, Kanal Abubakar Umar mai ritaya, Dakta Oby Ezekwesili, Farfesa Jibo Ibrahim, Yabagi Sanni; Ambasada Nkoyo Toyo, Isa Aremu, Farfesa Chidi Odinkalu, da Sanata Shehu Sani.

Ragowar 'yan kwamitin sun hada da; Farfesa Remi Sonaiya, Mallam Tanko Yunusa, Alhaji Shettima Yerima, Lady Funke Awolowo, Peter Ameh, Ogbeni Manre Banjo da sauransu.

Kungiyar za ta fito fili ta bayyana kanta a wannan wata na Yuli.

KARANTA KUMA: 'Yan takara 7 na jam'iyyar PDP na neman kujerar marigayi Sanata Osinowo

Daga cikin shawarwarin da kungiyar ta yanke sun hadar da neman magoya baya daga duk wani kwararo da sako na kasar masu akidar kawo sabbin sauye-sauye a tsarin siyasa da jagoranci domin ci gaban kasa.

Haka kuma, kungiyar za ta mayar da hankali wajen bunkasa tattalin arziki da ci gaba al'umma da aminci a tsakaninsu kamar yadda babi na biyi a kundin tsarin mulkin kasa ya yi tanadi.

Mambobin kungiyar sun kuma bayyana takaicinsu dangane da yadda gwamnatin kasar ta gaza bai wa al'umma kariya daga ta'addancin 'yan fashin da makami, 'yan daban daji da sauran masu tayar da kayar baya.

Sun kuma ce lokaci ya yi da ya kamata ‘yan Nijeriya su tashi su farga tare da yiwa kawunansu kartun ta nutsu wajen ceto kasar daga durkushewa sakamakon rashin shugabanci na gari.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel