Covid-19: 204 sun kamu a ranar Alhamis, Kano ta sha gaban Legas

Covid-19: 204 sun kamu a ranar Alhamis, Kano ta sha gaban Legas

Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta sanar da cewa karin sabbin mutane 204 ne aka tabbatar da cewa kwayar cutar covid-19 ta harba a fadin Najeriya.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa kusan 12:00 na daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta fitar da jerin jihohi da jimillar ma su dauke da kwayar cutar a kowacce jiha kamar haka;

80-Kano

45-Lagos

12-Gombe

9-Bauchi

9-Sokoto

7-Borno

7-Edo

6-Rivers

6-Ogun

4-FCT

4-Akwa Ibom

4-Bayelsa

3-Kaduna

2-Oyo

2-Delta

2-Nasarawa

1-Ondo

1-Kebbi

Alkaluman ma su dauke da kwayar cutar covid-19 da NCDC ta fitar a ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, sun nuna cewa jihar Kano, a karo na farko, ta sha gaban jihar Legas a yawan adadin mutanen ta su ka kamu da cutar.

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, akwai jimillar mutane 1932 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.

DUBA WANNAN: Gwamnan Bauchi ya amince da amfani da wasu kwayoyi 2 domin maganin cutar covid-19

An sallami mutane 319 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 58.

Alkaluman wadanda annobar covid-19 ta harba da NCDC ke fitarwa a 'yan kwanakin baya bayan nan na nuni da cewa annobar tana kara karfi a arewacin Najeriya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng