Covid-19: 204 sun kamu a ranar Alhamis, Kano ta sha gaban Legas
Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta sanar da cewa karin sabbin mutane 204 ne aka tabbatar da cewa kwayar cutar covid-19 ta harba a fadin Najeriya.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa kusan 12:00 na daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta fitar da jerin jihohi da jimillar ma su dauke da kwayar cutar a kowacce jiha kamar haka;
80-Kano
45-Lagos
12-Gombe
9-Bauchi
9-Sokoto
7-Borno
7-Edo
6-Rivers
6-Ogun
4-FCT
4-Akwa Ibom
4-Bayelsa
3-Kaduna
2-Oyo
2-Delta
2-Nasarawa
1-Ondo
1-Kebbi
Alkaluman ma su dauke da kwayar cutar covid-19 da NCDC ta fitar a ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, sun nuna cewa jihar Kano, a karo na farko, ta sha gaban jihar Legas a yawan adadin mutanen ta su ka kamu da cutar.
NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, akwai jimillar mutane 1932 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.
DUBA WANNAN: Gwamnan Bauchi ya amince da amfani da wasu kwayoyi 2 domin maganin cutar covid-19
An sallami mutane 319 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 58.
Alkaluman wadanda annobar covid-19 ta harba da NCDC ke fitarwa a 'yan kwanakin baya bayan nan na nuni da cewa annobar tana kara karfi a arewacin Najeriya.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng