Covid-19: 196 sun kamu a Najeriya, 24 a Kano, 18 a Gombe, 17 a Kaduna da suransu

Covid-19: 196 sun kamu a Najeriya, 24 a Kano, 18 a Gombe, 17 a Kaduna da suransu

Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta sanar da cewa karin sabbin mutane 196 ne aka tabbatar suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa kusan 12:00 na daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta fitar da jerin jihohi da jimillar ma su dauke da kwayar cutar a kowacce jiha kamar haka;

87-Lagos

24-Kano

18-Gombe

17-Kaduna

16- Abuja (FCT)

10-Katsina

8-Sokoto

7-Edo

6-Borno

1-Yobe

1-Ebonyi

1-Adamawa

Legit.ng ta lura cewa an samu karin mutum daya a kan adadin mutane 195 da NCDC ta bayyana cewa sun kamu da kwayar cutar a ranar Laraba, 29 ga watan Afrilu.

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Laraba, 29 ga watan Afrilu, akwai jimillar mutane 1728 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.

DUBA WANNAN: A karshe, sojojin Najeriya sun kwace kauyen Bula Shatane, 'yan Boko Haram sun mika wuya

An sallami mutane 307 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 51.

Alkaluman ma su kamuwa da NCDC ke fitarwa a 'yan kwanakin nan na nuni da cewa annobar tana kara karfi a arewacin Najeriya.

Kwamishinan lafiya a jihar Borno, Dakta Salihu Kwayabura, ya ce alamu sun nuna cewa kwayar cutar covid-19 ta yadu a tsakanin jama'a. Ya ce akwai bukatar bullo da dabarun binciko wadanda annobar ta harba.

Ya bayyana hakan ne ranar Laraba yayin taron da ya saba yi da manema labarai a kullum domin bayar da bayanai a kan halin da ake ciki dangane da yaki da annobar covid-19 a jihar Borno.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng