An rubuta kalaman kyamar musulunci a jikin wani masallaci a London

An rubuta kalaman kyamar musulunci a jikin wani masallaci a London

- A wani gini dake da kusanci da wani masallaci dake Kudancin birnin London ne aka zana taken da ke nuna kyama ga addinin Musulunci

- Jami'an tsaron yankin sun ce ana aiki da karamar hukumar Lambeth domin cire kalaman daga wajen

- Magajin garin London ya wallafa cewa, babu shakka za a gano wadanda suka yi wannan aika-aikar kuma za su fusknaci hukunci

A wani gini dake da kusanci da wani masallaci ne da ke Kudancin birnin London aka zana taken da ke nuna kyama ga addinin Musulunci.

An gano wannan alamar ne a jikin wani gini a kusa da cibiyar addini dake kan titin Brixton da karfe 11:00 agogon GMT.

Jami'an tsaron yankin sun ce suna aiki da karamar hukumar Lambeth domin cire "kalaman batancin" daga jikin ginin da gaggawa ba tare da bata lokaci ba.

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: Soja mafi tsufa a Najeriya ya rasu yana da shekara 101 (Hotuna)

Hukumar 'yan sandan ta kara da cewa, tana gudanar da bincike don gano wanda yake da hannu a wannan aika-aikar.

Sadiq Khan ya ce, bai ji dadin ganin rubutun ba wanda aka manna a ginin bayan kwanaki kadan da aka manna kalaman batanci ga Yahudawa, a shaguna da wurin ibadar Yahudawan a Arewacin birnin London.

Magajin garin London ya wallafa hakan a shafinsa na kafar sada zumuntar zamani ta Twitter. Ya ce: "Duk kalaman nuna wariya, alama ce ta tsoro kuma masu laifin zasu fusknaci fushin hukuma."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164