Mahaifina na lalata dani tun ina 'yar shekara 18, yanzu haka 'ya'yana guda biyu duk na shi ne - Matar aure ta tona asiri

Mahaifina na lalata dani tun ina 'yar shekara 18, yanzu haka 'ya'yana guda biyu duk na shi ne - Matar aure ta tona asiri

- Wata mata 'yar kasar Ghana ta bayyana wani mummunan sirri da ya kada duk wanda ya karanta

- Matar ta bayyana irin alakar dake tsakaninta da mahaifinta

- Inda ta ce yana kwanciya da ita tun tana 'yar shekara 18, kuma 'ya'yanta guda biyu da ta haifa ma na shi ne

Wata mata 'yar kasar Ghana ta bayyana wani sirri wanda ya girgiza kowa da kowa, matar dai tayi magana ne a wani shafi na kasar Ghana mai suna GHOne, inda tace ta sha yin jima'i da mahaifinta da ya haifeta.

Matar wacce yanzu haka tace tayi aure har yara guda biyu, ta ce ta fara kwanciya da mahaifinta tun tana 'yar shekara 18 a duniya, kuma har yanzu da tayi aure ta haifi yara guda biyu ta kasa daina wa.

Matar ta cigaba da cewa a lokacin da mahaifiyarta taji labarin wannan abu dake tsakaninta da mahaifinta ta razana sosai, hakan yasa ta fita har yanzu ba a san inda take ba.

KU KARANTA: Babbar magana: Za a fara koyawa yara 'yan shekara 4 ilimin jima'i a makarantar firamare a kasar Ghana

Wani babban abin tsoro da ta fada shine, yanzu haka yara guda biyu da take dasu ba na mijinta bane 'ya'yan mahaifinta ne.

Matar ta rubuta wannan abu ne inda take neman taimako bayan ta bayyana cewa ta gaji da wannan abu da take yi tana so karshen alakarta da mahaifinta yazo.

Ta cigaba da cewa mijinta mutumin kirki ne wanda bai kamata ta dinga yi mishi irin wannan cin amanar ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng