Ngige, Malami da sauran ministoci 10 da zasu maimaita mukamansu a zango na biyu
A wa'adin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na biyu, ministoci 12 ne cikin 43 aka samu za su maimaita mukaman da suka rika a zango na farko. An rantsar da sabbin ministocin a ranar Laraba, 21 ga watan Agustan 2019.
Shugaban kasa Buhari a ranar Laraba cikin fadarsa ta Villa da ke birnin Abuja, ya rantsar da sabbin ministoci 43 da zasu jagoranci ma'aikatu a kasar inda kowanen su ya san makamar aikinsa.
Bayan sake dawowa karo na biyu, ministoci 12 ne aka samu za su maimata kujerun da suka jagoranta a wa'adin gwamnatin Buhari na farko. Ministoci tare da ma'aikatu gami jihohinsu sune kamar haka:
1. Anambra: Chris Ngige - Ministan Kwadago da samar da aiki
2. Ribas: Rotimi Amaechi - Ministan Sufuri
3. Katsina: Hadi Srika - Ministan Sufurin Jiragen Sama
4. Enugu: Geoffery Onyeama - Ministan harkokin kasashen ketare
5. Jigawa: Suleiman Adamu - Ministan Ruwa
6. Adamawa: Muhammad Musa Bello - Ministan Birnin Tarayya
7. Bauchi: Adamu Adamu - Ministan Ilimi
KARANTA KUMA: Sake kama Wadume za ta kore duk wani shakku - DHQ
8. Ebonyi: Ogbonnaya Onu - Ministan Kimiyya da Fasaha
9. Kaduna: Zainab Shamsuna Ahmed - Ministar Kudi
10. Kwara: Lai Muhammad - Ministan Labarai da Al'adu
11. Kebbi: Abubakar Malami - Ministan Shari'a
12. Legas: Babutunde Fashola - Ministan Ayyuka da Gidaje (Sai dai a yanzu an rage masa nauyin ma'aikatar makamashi).
Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
https://facebook.com/legitnghausa
https://twitter.com/legitnghausa
Asali: Legit.ng