Ngige, Malami da sauran ministoci 10 da zasu maimaita mukamansu a zango na biyu

Ngige, Malami da sauran ministoci 10 da zasu maimaita mukamansu a zango na biyu

A wa'adin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na biyu, ministoci 12 ne cikin 43 aka samu za su maimaita mukaman da suka rika a zango na farko. An rantsar da sabbin ministocin a ranar Laraba, 21 ga watan Agustan 2019.

Shugaban kasa Buhari a ranar Laraba cikin fadarsa ta Villa da ke birnin Abuja, ya rantsar da sabbin ministoci 43 da zasu jagoranci ma'aikatu a kasar inda kowanen su ya san makamar aikinsa.

Bayan sake dawowa karo na biyu, ministoci 12 ne aka samu za su maimata kujerun da suka jagoranta a wa'adin gwamnatin Buhari na farko. Ministoci tare da ma'aikatu gami jihohinsu sune kamar haka:

1. Anambra: Chris Ngige - Ministan Kwadago da samar da aiki

2. Ribas: Rotimi Amaechi - Ministan Sufuri

3. Katsina: Hadi Srika - Ministan Sufurin Jiragen Sama

4. Enugu: Geoffery Onyeama - Ministan harkokin kasashen ketare

5. Jigawa: Suleiman Adamu - Ministan Ruwa

6. Adamawa: Muhammad Musa Bello - Ministan Birnin Tarayya

7. Bauchi: Adamu Adamu - Ministan Ilimi

KARANTA KUMA: Sake kama Wadume za ta kore duk wani shakku - DHQ

8. Ebonyi: Ogbonnaya Onu - Ministan Kimiyya da Fasaha

9. Kaduna: Zainab Shamsuna Ahmed - Ministar Kudi

10. Kwara: Lai Muhammad - Ministan Labarai da Al'adu

11. Kebbi: Abubakar Malami - Ministan Shari'a

12. Legas: Babutunde Fashola - Ministan Ayyuka da Gidaje (Sai dai a yanzu an rage masa nauyin ma'aikatar makamashi).

Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng