Yan Shi’a sun sha alwashin dawo da zanga-zanga, sun nemi sanin inda El-Zakzaky yake

Yan Shi’a sun sha alwashin dawo da zanga-zanga, sun nemi sanin inda El-Zakzaky yake

Mabiya kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN), wacce aka fi sani da Shi’a, sun sha alwashin dawo da zanga-zangarta na yau da kullun a kasar, sakamakon takunkumin da gwamnatin Najeriya ta sanya wa shugabansu, Sheikh Ibahim El-Zakzaky bayan ya je kasar Indiya yin magani.

Kungiyar ta kuma yi Allah wadai da yadda aka yi wa Shugaban nasu da kuma tafiya dashi da jami’an DSS suka yi, a lokacin da ya isa filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe International Airport, Abuja, zuwa wani wuri da ba a sani ba a ranar Juma’a, 16 ga watan Agusta.

A wani jawabi dauke da sa hannun kakakin kungiyar, Ibrahim Musa, mabiya El-Zakzaky sun bayyana cewa za su ci gaba da zanga-zangarsu domin tursasa gwamnati bin umurin kotun Kaduna da ta bukaci a sake shi domin zuwa yin magani.

Kungiyar ta bayyana cewa mahukuntan Najeriya sun nuna cewa hankalinsu bai kwanta da damar da aka ba shugabansu na zuwa neman magani a wajen kasar ba.

KU KARANTA KUMA: Ahmad Lawan ya jagoranci shugabannin majalisar dattawa zuwa wajen Buhari a Daura

A baya mun ji cewa kungiyar Shia ta Najeriya, IMN, ta zargi gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari da kokarin halaka shugabanta, Ibrahim Zakzaky yayin da ya tafi jinya a kasar Iran ne, inji rahoton jaridar Daily Nigerian.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito Kaakakin kungiyar, Ibrahim Musa ne ya bayyana haka a ranar Juma’a, inda yace gwamnatin ta yi kokarin yin amfani da kawayenta na kasashen waje ne wajen kashe Zakzaky a Indiya, amma suka gano.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng