Ka aure ni ko na kashe kaina - Bidiyon Budurwar da ta dinga suma tana rokar saurayinta ya aureta

Ka aure ni ko na kashe kaina - Bidiyon Budurwar da ta dinga suma tana rokar saurayinta ya aureta

- Wata budurwa ta kunyata kanta da saurayinta a kan wani babban titi na jihar Legas

- Budurwar ta suma yafi a kirga inda take rokar saurayinta akan ya taimaka ya aureta ko kuma ta kashe kanta

- Yayin da budurwar ke faman barka kuka akan saurayin, shi kuma saurayin yana ganin yaudarece da damfara budurwar ke son yi masa

Wata budurwa ta kunyata kanta da saurayinta a kan wani titi a jihar Legas, yayin da ta dinga birgima tana suma tana kuma rokar shi akan ya aureta ko kuma ta kashe kanta.

A wani da ya fara yawo a shafukan sada zumunta na zamani, ya nuna yadda budurwar take ta faman suma akan wata babbar hanya inda take yin magana cikin harshen turanci take cewa: 'Marry me or i die' ma'ana "Ka aure ni ko na kashe kaina."

KU KARANTA: To fah: Maza ne suke jawo yawan sake-saken da ke faruwa a kasar Hausa - Wani mutumi ya bayar da dalilanshi

Yayin da shi kuma wani matashi da aka hasko yana kuka shima yana cewa:

"Wannan yarinyar za ta sanya ni cikin matsala, wannan wane irin abu ne haka, wacc irin damfara ce kike yi haka," yayin da su kuma mutane suka taru a kansu suna kallon ikon Allah.

A yayin da mutane da yawan gaske suke ganin cewa soyayya a wannan lokaci batawa kai lokaci ce, ita kuma budurwar a lokacin take suma saboda tsananin soyayya da kaunar da take yiwa saurayin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng