Gadar miliyan N700 da Kwankwaso ya gina a Kano ta tsage
Gadar kasa ta unguwar Gadon Kaya da tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya gina a kan miliyan N700 ta tsage.
Ruftawar da gadar ta yi ya jefa masu ababen hawa a cikin wahala saboda rufe hanyar da hukuma ta yi.
Gadar, wacce ke sada masu ababen hawa da jami'ar Bayero da ke Kano, ta rufta ne ranar Lahadi.
A Cewar wani rahoto da gwamnatin jihar Kano ta fitar ranar Talata, saman gadar ya tsage tare da ruftawa sakamakon ruwan sama da aka sha a garin Kano a daren ranar Lahadi, lamarin da ya jawo aka hana ababen hawa bi ta hanyar gaba daya.
An rufe hatta hannu daya na gadar da bai rufta ba, wanda zai kai masu ababen hawa zuwa Kofar Famfo.
DUBA WANNAN: Dubun dan fashi da ke buya a cikin kabari ta cika
Kwankwaso ya gina gadar ne a kan miliyan N700 a zangon mulkinsa na biyu daga 2011 zuwa 2015.
Kamfanin gine-gine na Rocard ne ya yi kwangilar aikin gadar wacce Kwana sa ya saka wa suna 'Gadar Prince Abubakar Audu'.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng