Yanzu Yanzu: Osinbajo ya shilla kasar Rwanda

Yanzu Yanzu: Osinbajo ya shilla kasar Rwanda

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya bar babban birnin tarayya Abuja domin zuwa kasar Ruwanda.

Osinbajo zai wakilci shugaban kasa Muhammadu Buhari ne a wurin taron bikin cikar kasar Rwanda shekaru 25 da samun 'yan ci wanda za a gudanar a ranar Alhamis 4 ga watan Yulin 2019.

Hakan na dauke ne cikin jawabin da hadiminsa na fannin kafafen yada labarai, Mr Laolu Akande ya fitar inda ya ce, " Farfesa Osinbajo zai hadu da sauran shugaban kasahen Afirka a wurin taron da ake sa ran gudanarwa a ranar Alhamis 4 ga watan Yuli a Kigali domin tuna kawo karshen kisar kare dangi da akayi a kasar a 1994.

DUBA WANNAN: Magajin Garin daura: 'Yan sanda sun kama wadanda suka yi garkuwa da shi, sun samu alburusai

"Wasu manyan jami'an gwamnati za su yi wa mataimakin shugaban kasar rakiya zuwa taron."

Ana sa ran zai dawo gida Najeriya a ranar Alhamis 4 ga watan Yulin 2019.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164