Gwamna El-Rufai na shirin sanar da jerin sunayen sabbin kwamishinoninsa
- Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya shirya tsaf domin gabatar da jerin sunayen sabon majalisarsa a gaban Majalisan dokokin jihar
- Wata majiya ta bayyana cewa El-Rufai zai gabatar da sunayen tsakanin yau Talata, 2 ga watan Yuli da kuma gobe Laraba, 3 ga watan Yuli
- Majiyar ta tattaro cewa majalisarsa za ta kunshi matasa da ya dade yana ba horo na musamman
Rahotanni sun kawo cewa Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya shirya tsaf domin gabatar da jerin sunayen sabon majalisarsa a gaban Majalisan dokokin jihar.
Wata majiya mai inganci a majalisar dokokin jihar ce ta tabbatar ma da jatidar Daily Trust daren jiya Litinin, 1 ga watan Yuli cewa suna sa ran samun jerin sunayen tsakanin yau Talata ko gobe Laraba.
A cewar majiyar wanda ya neMi a sakaya sunansa, yace sunayen sun hada da na matasa wadanda gwamnan ya ba horo a shekarun da suka gabata.
Majiyar ta kara dacewa daga abunda ya tattaro, bayan majalisar ta gama tantance sunayen, Gwamna El-Rufai zai tura su ma’aikatu da kuma mukamai a ofishin sa.
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari yayi sabon nadi mai muhimmanci
“Ga dukkan alamu Kwamishinoni masu kwazo ne kawai za su dawo, yayinda wasu jami’ai za su zamo cikakkun kwamishinoni daga mukamin shugabanni a wasu hukumomi,” inji majiyar.
Ya kara da cewa a halin yanzu hukumomin tsaro suna aiki akan wasu daga cikin sunayen.
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.
Asali: Legit.ng