Sanusi ya tsige Limamin wani masallacin Juma’a

Sanusi ya tsige Limamin wani masallacin Juma’a

-Sarkin Kano ya cire babban limamin masallacin Juma'an Limawa

-Sarki Sanusi ya tsige limamin ne sakamakon bijirema umarninsa kan sha'anin ganin watan sallar idi da ya yi har sau biyu

-Limamin da aka ciren dai sunansa Salihu Muhammad wanda kuma yaki cewa komi a kan maganar yayin da 'yan jarida suka nemi jin ta bakinsa

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi Lamido na biyu a ranar Juma’a ya bayar da umarnin tsige babban limamin masallacin Juma’an Limawa dake karamar hukumar Kumbotso a jihar, Malam Salihu Muhammad.

Tuni dakatar da wannan limami ya fara aiki ba tare da bata lokaci ba. Muhammad dai, ana zarginsa ne da sabawa umarnin Sarki a kan ganin watan sallar idi. Abinda wannan limamin ya aikata kuwa shi ne, bai ajiye azumi ranar da aka ga wata ba said a ya kara kwana daya bayan ya ga watan da idonsa sannan ya jagoranci ta shi sallar idin.

KU KARANTA:Duk tsuntsun da ya ja ruwa: Kasar Iran ta gargadi Trump a kan maganar yaqi

Sanusi ya bayyana cewa ba yanzu limamin ya fara wannan dabi’a ba, ko a shekarar da ta gabata ya aikata irin wannan abu.

Haka zalika, ya nuna cewa, tunda har dai limamin ya zama mai kunnen kashi ta hanyar maimaita laifin da aka gargadeshi a kai, to ya zama wajibi a sauya shi da wani daban.

‘Yan jarida sun tuntubi limamin da aka tsigen domin jin ta bakinsa amma abin ya gagara.

A wani labarin mai kama da wannan, mun ji cewa Sarki Muhammadu Sanusi Lamido na II ya yabawa Shugaban kasa Muhammadu Buhari kan yadda yake bada himma wurin yaki da talauci a kasar nan.

Sarkin yayi wannan jawabin ne wurin wani taro na musamman da aka gudanar a jiharsa ta Kano, a karkashin ofishin babban ma'ajin gwamnatin tarraya.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng