Rundunar sojin sama ta lalata hedikwatar tsare-tsaren kungiyar ISWAP a Kollaram, Borno
Rundunar sojin saman Najeriya (NAF) ta bayyana cewa dakaruta dake gudanar da aikin Operation Lafiya dole sun tarwatsa hedikwatan tsare-tsare na kungiyar yan ta’addan ISWAP a Kollaram da ke yankin Arewacin Borno.
Air Commodore Ibikunle Daramola, Darektan Sadarwa da yada labarai na NAF, ya bayyana haka a wani jawabin da ya gabatar a ranar Alhamis, 27 ga watan Yuni, a Abuja.
Kakakin rundunar ya bayyana cewa dakarunta sun gudanar da aikin ne a ranar Laraba, 26 ga watan Yuni.
“Rundunar Sojin saman Najeriya (NAF), ta hannun Air Task Force (ATF) na Operation lafiya dole, ta kaddamar OPERATION GREEN SWEEP 2 akan kungiyar yan ta’addan a yankin Arewa maso gabashin kasar.
“Aikin rundunar sojin saman da aka fara a ranar Laraba, 26 ga watan Yuni, zata zabi wurare a cikin yankin Arewa maso Gabas don cigaba da tarwatsa sauran yan ta’addan da sansaninsu.”
KU KARANTA KUMA: Ku fada mun kalubalen da kuke fuskanta a filin daga – Buratai ya bukaci sojoji
Kakakin rundunar yayi bayanin cewa an kaddamar da harin ne bayan rangaji daban-daban da sashin kwararru suka gudanar.
Yace binciken ya nuna bayyanar wasu adadi na mayakan ISWAP a gine-ginen da ke karkashin bishiyoyi da suka yadu a wajen da kuma wasu ramuka masu zurfi a wurare daban-daban.
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.
Asali: Legit.ng