Mata sun yi zanga-zanga akan hare-hare da kashe-kashen yan bindiga a Taraba
- Mata a Taraba sun gudanar da wani zanga-zanga akan hare-haren da aka kai jihar
- Matan sun koka kan kisan mazaje da yaransu
- Masu zanga-zangan sun kuma yi zargin cewa sojoji sn hana su sannan suka jima wasu rauni
Matan kauyen Kona da ke karamar hukumar Jalingo na jihar Taraba a ranar Talata, 18 ga watan Yuni sunyi zanga zanga akan hare-hare da kashe-kashen da yan bindiga suka yi kwanan nan a kauyensu.
Matan wadanda ke zanga zanga kan mutuwar mazajensu da yara a hare-haren sun mamaye titunan Kona Garu a Jalingo suka kuma kare a ATC.
Sun yi korafin cewa sun razana da harin da ake cigaba da daukakawa kamar yanda yan bindigan suka kai mamaya kauyukan kan babura inda suka yi harbe-harbe da kone-konen gidaje.
Har ila yau sun bukaci a saki matasansu cikin gaggawa wanda suke ikirarin yan sanda sun kama. Matan har ila yau sunyi zargin cewa Rundunan Soji ta katse zanga-zangan sannan suka ji ma wasu daga cikin su rauni.
Babban kwamandan bataliya na 20 Model, Serti, Laftanal Kanal Mohammed Adamu a hiran wayar talho, ya musanta zargin cewa mutanensa suna da hannu cikin zanga-zangan matan.
Kakakin rundunar yan sandan jihar, David Misal yace an samar da isasshen tsaro ga mata masu zanga zangan a lokacin da suka gudanar da zanga-zanga a tituna. Ya kara da cewa a halin yanzu an samar da zaman lafiya a kauyukan da lamarin ya shafa.
Har ila yau ya tabbatar da kamun wasu matasa wadanda suka mallaki makamai masu hatsari, inda ya kara da cewa a halin yanzu ana kan gudanar da bincike.
KU KARANTA KUMA: Boko Haram ta na bada agajin abubuwan more rayuwa saboda sakacin Gwamnati - Rabaren Manoso
Mutanen kauyen sunyi ikirarin cewa an kashe akalla mutane takwas a hare-haren da ya shafi kauyuka a Kona da ATC wanda aka fara daga daren Lahadi zuwa safiyar Litinin.
Gwamnatin jihar ta kafa dokar hana fita daga safe zuwa dare a yankunan da lamarin ya shafa.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng