Zango na biyu: Shugaba Buhari zai yi sallar Juma’a a babban masallacin kasa a yau

Zango na biyu: Shugaba Buhari zai yi sallar Juma’a a babban masallacin kasa a yau

A yau Juma’a, 24 ga watan Mayu, Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai gabatar da sallar Juma’a a babban masallacin kasa, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Shugaban kasar zai gabatar da sallar Juma’a a masallacin ne daga cikin tsare-tsare da aka shirya na rantsar da shi a karo na biyu.

Za a rantsar da shugaba Buhari a karo na biyu a ranar Laraba, 29 ga watan Mayu a dakin taro na Eagle Square da ke birnin tarayya, Abuja.

Zango na biyu: Shugaba Buhari zai yi sallar Juma’a a babban masallacin kasa a yau
Zango na biyu: Shugaba Buhari zai yi sallar Juma’a a babban masallacin kasa a yau
Asali: Facebook

Idan za a tuna yan shekarun baya, Shugaban kasar ya daina yin sallar Juma’a a babban masallaccin kasar. Shugaban kasar yayi bayanin cewa hukunci ya kasance ne domin guje ma takurar da zirga-zirgan Shugaban kasa zai haddasa wa mutane.

Shugaban kasar kan gudanar da sallar Juma’a ne a masallacin fadar Shugaban kasa.

KU KARANTA KUMA: Gwamna Masari ya soke bikin ranar 29 ga watan Mayu

A baya Legit.ng ta ruwaito cewa Gwamnatin tarayya a ranar Litinin, 20 ga watan Mayu, ta kaddamar da ranar Laraba, 29 ga watan Mayu da kuma 12 ga watan Yuni a matsayin ranakun hutu domin bikin rantsar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma ranar Damokradiyya.

Ministan labarai, Alhaji Lai Mohammed ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai gabannin rantsar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari a karo na biyu.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng