Shugaban kasar Koriya ta Kudu ya taya shugaba Buhari murnar samun nasarar tazarce

Shugaban kasar Koriya ta Kudu ya taya shugaba Buhari murnar samun nasarar tazarce

Shugaban kasar Koriya ta Kudu, Moon Jae-in, ya taya shugaban kasa Muhammadu Buhari murnar samun nasarar tazarce yayin zaben kasa da aka gudanar a ranar 23 ga watan Fabrairun 2019.

Mai magana da yawun shugaban kasa Buhari, Mallam Garba Shehu, shi ne ya bayyana hakan a yau Talata yayin ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa ta Villa da ke garin Abuja.

Mallam Shehu ya ce, shugaban kasa Jae-in cikin wata rubutacciyar wasika da ya aike da ita a madadin sa da kuma al'ummar kasar Koriya ta Kudu, ya taya shugaban kasa Buhari murnar samun nasarar tazarce.

Shugaban kasar Koriya ta Kudu ya taya shugaba Buhari murnar samun nasarar tazarce
Shugaban kasar Koriya ta Kudu ya taya shugaba Buhari murnar samun nasarar tazarce
Asali: Facebook

Cikin wasikar sa shugaba Jae-in ya yi fatan Najeriya za ta samu kyakkyawar makoma ta ci gaba musamman a fannin habakar tattalin arziki a karkashin jagorancin shugaban kasa Buhari.

KARANRA KUMA: Atiku ya shigar da manyan korafi 5 domin kalubalantar sakamakon zabe

Ya bayyana farin cikin sa dangane da yadda Najeriya da kasar Koriya ta Kudu ke ci gaba da cin moriyar kyakkyawar alaka a tsakanin su gami da hadin kai tun a shekarar 1980.

Shugaba Jae-in ya yi fatan son barka da kuma arziki na lafiya ga shugaban kasa Buhari a yayin da daura damarar tabbatar da kyakkyawar makoma a jamhuriyyar Najeriya.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na dandalan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel