Sakamakon zabe: hadimin Ganduje ya yi murabus saboda Abba Gida-Gida
Alhaji Hashim Suleiman, babban mai bawa gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, shawara a kan raya birane, ya mika takaradar sa ta yin murabus daga mukamin sag a sakataren gwamnatin jihar Kano a yau, Laraba.
A takardar sa ta yin murabus din, ya bayyana cewar dalilinsa na dauka wannan mataki shine saboda gwamna Ganduje ya ki amincewa da kayen da dan takarar gwamnan jihar Kano a jam’iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf, ya yi ma sa.
Suleiman ya ce Abba ne ya lashe zaben na ranar Asabar da hukumar zabe ta kasa (INEC) ta bayyana a atsayin wanda bai kammalu ba.
A takardar da Suleiman ya rubuta da hannun sa, y ace: “na rubuta wannnan takarda ne domin sanar da kai cewar na ajiye mukamina na bayar da shawara a kan raya birane bisa radin kai na.
DUBA WANNAN: Cakwakiya: Sanarwar Orji Kalu ya ci zaben sanata a APC kuskure ne – INEC
“Ina mai godiya gare ka bisa damar ka bani na yin aiki a gwamnatin ka.”
Sannan ya kara da cewa kamata ya yi gwamnan da ke amsa sunan ‘Khadimul-Islam’ ya kasance mai rungumar kaddara da yarda da ikon Allah a duk halin da ya tsinci kan sa.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng