Sakamakon zabe: hadimin Ganduje ya yi murabus saboda Abba Gida-Gida

Sakamakon zabe: hadimin Ganduje ya yi murabus saboda Abba Gida-Gida

Alhaji Hashim Suleiman, babban mai bawa gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, shawara a kan raya birane, ya mika takaradar sa ta yin murabus daga mukamin sag a sakataren gwamnatin jihar Kano a yau, Laraba.

A takardar sa ta yin murabus din, ya bayyana cewar dalilinsa na dauka wannan mataki shine saboda gwamna Ganduje ya ki amincewa da kayen da dan takarar gwamnan jihar Kano a jam’iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf, ya yi ma sa.

Suleiman ya ce Abba ne ya lashe zaben na ranar Asabar da hukumar zabe ta kasa (INEC) ta bayyana a atsayin wanda bai kammalu ba.

Sakamakon zabe: hadimin Ganduje ya yi murabus saboda Abba Gida-Gida
Ganduje da Abba Gida-Gida
Asali: UGC

A takardar da Suleiman ya rubuta da hannun sa, y ace: “na rubuta wannnan takarda ne domin sanar da kai cewar na ajiye mukamina na bayar da shawara a kan raya birane bisa radin kai na.

DUBA WANNAN: Cakwakiya: Sanarwar Orji Kalu ya ci zaben sanata a APC kuskure ne – INEC

“Ina mai godiya gare ka bisa damar ka bani na yin aiki a gwamnatin ka.”

Sannan ya kara da cewa kamata ya yi gwamnan da ke amsa sunan ‘Khadimul-Islam’ ya kasance mai rungumar kaddara da yarda da ikon Allah a duk halin da ya tsinci kan sa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng