Ana cigaba da kirga kuri'un zaben Gwamna da 'Yan Majalisa a Kano

Ana cigaba da kirga kuri'un zaben Gwamna da 'Yan Majalisa a Kano

Mun samu labari cewa ana kirga kuri'u na zaben gwamna a jihar Kano da sauran jihohin Najeriya. Gwamna mai-ci zai samu kalubale daga jam’iyyun adawa irin su PDP da kuma jam’iyyar PRP.

Ga dai wasu daga cikin rahotannin da mu ke samu daga wasu kananan hukumomin na jihar ta Kano kawo yanzu.

1. Ungogo LG

PDP= 42, 032

APC= 26, 118

2. Rano LG

APC 16, 694

PDP 14, 892

3. Madobi LG

APC= 24, 491

PDP= 24, 309

KU KARANTA: PDP ta nemi a cafke Mukarraban Ganduje bayan sun yi ikirarin lashe zabe

4. Kibiya LG

PDP= 17, 373

APC= 15, 760

5. Bebeji LG

PDP= 18, 533

APC=17, 418

6. Gezawa LG

PDP 24, 151

APC 20, 506

KU KARANTA: An yi awon gaba da kayan aikin zaben Gwamna a Kudu

7. Albasu LGA

APC 25,358

PDP 18,441

8. Bebeji LG

APC. 17,418

PDP. 18,533

9. BUNKURE LG

APC 20,407

PDP 20,222

10. Rimin Gado

APC 19,453

PDP 13,777

KU KARANTA: Yadda sakamakon zaben sabon Gwamna a Jihar Kaduna yake kasancewa

Tuni dai gwamna Abdullahi Ganduje da Mai dakin sa watau Hajiya Dr. Hafsat Umar Ganduje su ka kada kuri’ar su a zaben na yau. Haka shi ma ‘Dan takarar jam’iyyar PRP, Salihu Takai ya kada ta sa kuri’ar a mazabar sa.

Kamar yadda mu ka ji an samu takaddama a yankin Mandawari inda magoya bayan ‘dan takarar PDP watau Abba Kabir Yusuf su ka hadu da Mabiyan APC da ke tare da shugaban jam’iyya na jihar watau Abbas Sanusi.

Zaben Kano: An damke mota da kayan zabe a Yankin Mataimakin Ganduje
Abba Yusuf da Ganduje sun yi zabe yayin da aka kama kayan zabe a Kano
Asali: UGC

Kwamishin ‘yan sanda na jihar Kano watau Muhammad Wakili ya kawo ziyarar ba-zata zuwa Yankin na Mandawari da ke cikin birnin Kano domin ganin an yi zabe lafiya. Akwai dai manyan ‘yan siyasan Kano a yankin.

Haka kuma mun ji cewa dazu nan Jami’an tsaro su kayi nasarar damke wata mota cike makil da kayan zabe a wata makaranta da ke Magwan da ke cikin Yankin Gawuna inda Mataimakin Gwamnan jihar Kano mai-ci ya fito.

Ana kukan cewa ana amfani da kudi wajen sayen kuri’un jama’a yayin da a wasu wurare kuma ake kukan cewa ba a kai isassun kayan zaben da ake bukata ba kamar yadda mu ke samun labari.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel