Buhari ya sha gaban Atiku Abubakar a halin da ake ciki a Gombe

Buhari ya sha gaban Atiku Abubakar a halin da ake ciki a Gombe

Dan takarar shugabancin kasa a karkashin inuwar jam’iyyar APC, Muhammadu Buhari ne ke kan gaba a iya sakamakon zaben shugaban kasa da hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta sanar a jahar Gombe, inda Atiku ke binsa a baya.

Legit.ng ta ruwaito zuwa yanzu an sanar da sakamakon zabe na kananan hukumomi guda tara cikin kananan hukumomin jahar guda goma sha daya, inda a yanzu Buhari ke jan gora a kananan hukumomi guda bakwai, Atiku kuma yana da biyu.

KU KARANTA: Albarkacin kaza: Dan yayar Buhari ya yi biji biji da jam’iyyar PDP a takarar dan majalisa

Kafatanin kuri’un da Buhari ya samu a iya kananan hukumomi guda taran da aka sanar da sakamakonsu shine dubu dari uku da daya da dari shida da saba’in da bakwai, yayin da Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u dubu dari da goma da dari biyu da shirin da tara, 110, 229.

Sauran kananan hukumomi biyu da ba’a sanar da sakamakonsu ba sun hada da Akko da Funakaye, amma ga jerin sakamakon kananan hukumomin da aka sanar guda tara:

Balanga:APC – 29, 697, PDP- 14, 614

Billiri: APC – 15, 331, PDP – 21, 328

Dukku: APC – 32, 010, PDP – 7, 437

Gombe: APC – 86, 162, PDP – 7, 634

Kwami: APC – 36, 317, PDP – 6, 614

Nafada: APC – 15, 417, PDP – 5, 792

Kaltungo: APC – 20, 944, PDP – 20, 733

Shomgom: APC – 9, 642, PDP – 12, 871

Yamaltu Deba: APC 56, 157, PDP – 13, 208

A wani labarin kuma, gwamnan jahar Gombe, Ibrahim Hassan Dankwambo ya fadi warwas a kokarinsa na haurawa majalisar dattawa a inuwar jam'iyyar PDP, inda dan takarar APC Saidu Alkali ya lallasashi.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel