Kamfe: Atiku ya gigita al'ummar jihar Kano
Mun samu cewa a yau Lahadi, 10 ga watan Fabrairu, 2019, dan takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya gudanar da yakin neman zaben sa cikin salo a jihar Kano ta Dabo Tumbin Giwa.
Ko shakka ba bu birnin Kano ya cika ya batse yayin da magoyo baya tamkar ridi suka yi turuwa sanye da jajeyen huluna domin yiwa Wazirin Adamawa kyakkyawar tarba da bai samu makamanciyar ta ba a duk ilahirin jihohin Najeriya.
Bayan dirar Atiku a safiyar yau ta Lahadi tare da jiga-jigan jam'iyyar PDP na kasa da suka hadar da shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki da kuma shugaban jam'iyyar na kasa, Prince Uche Secondus, sun kuma kama hanyar su ta kai ziyarar ban girma fadar Mai Martaba San Kano, Muhammadu Sanusi II.
Alkaluman siyasa sun tabbatar da cewa, Atiku ya samu goyon bayan al'ummar jihar Kano a sakamakon rawar da tsohon gwamnan jihar ya taka, Sanata Rabi'u Kwankwaso, da aka yiwa lakabi da madugu uban tafiya.
KARANTA KUMA: APC-ta-shiga-rudu: Shugaba Buhari ya kasa daga hannun dan takara a jihar Zamfara
Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:
https://facebook.com/legitnghausa
https://twitter.com/legitnghausa
Asali: Legit.ng