Yanzu-yanzu: An nada Bashir a matsayin shugaban riko na NPC
Gwamnatin tarayya ta amince da nadin Alhaji Hassan Bashir a matsayin shugaban riko na Hukumar Kidayar Jama'a ta Kasa wato National Population Commission.
Sanarwar da ta fito daga Direkta Janar na Hukumar, Dr Ghaji Ismaila Bello a ranar Juma'a a Abuja ta nuna cewa an sanar da nadinsa ne cikin wata wasika mai dauke da sa hannun Sakataren gwamnatin tarayya kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Source: Twitter
DUBA WANNAN: Kiristoci ne suka taimake ni lokacin da musulmi suka juya min baya - Buhari
Nadin na sa yana zuwa ne bayan karewar wa'addin tsohon shugaban hukumar, Eze Duruiheoma a ranar 23 ga watan Janairun 2019.
Bashir zai rika kula da ayyukan hukumar har zuwa lokacin da za a nada sabon shugaba. A halin yanzu dai shine ma'aikaci mafi girma a hukumar.
"Kafin nadinsa, Alhaji Hassan Bashir shi ne Kwamishina da ke wakiltan Jihar Bauchi a hukumar ta Kidayar," inji sanarwar
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng