Rikakken Malamin coci a Anambra ya ba Shugaba Buhari nasara a zaben 2019

Rikakken Malamin coci a Anambra ya ba Shugaba Buhari nasara a zaben 2019

Mun ji labari cewa wani Malamin addinin kirista wanda yayi kaurin-suna ya bayyana cewa jam’iyyar APC mai mulki ta Shugaba Muhammadu Buhari ce ta za tayi nasara a babban zaben da za ayi a bana.

Wani rikakken Malamin coci a Anambra ya ba Shugaba Buhari nasara a zaben 2019
Wani Fasto a Anambra yace Jam’iyyar APC za ta doke PDP
Asali: Depositphotos

Kamar yadda mu ka ji labari daga jaridar Pulse ta kasar nan, Dr Ramas Azuzu, ya gano cewa APC ce za ta sake lashe zaben 2019. A harsashen wannan babban malamin, Buhari zai doke Abokan hamayyar sa irin su Atiku Abubakar.

Babban Faston kuma Jagoran cocin nan na Liberation Temple of the Absolute God, ya bayyana wannan ne lokacin da yake magana da wasu ‘yan jarida a Ranar Lahadin nan da ta gabata a cikin garin Anaocha da ke jihar Anambra.

KU KARANTA: An bankado wata makarkashiyar Boko Harm daf da zaben 2019

Shehin Malamin ya kuma bayyanawa jama’a cewa akwai yiwuwar rikici ya barke bayan zaben don haka yayi kira a yawaita addu’o'i. Wannan malami na kirista dai yace da yayi na sa duban, an nuna masa cewa Buhari ne zai ci zabe.

Babban Faston ya kuma yabawa gwamnatin Buhari wanda a cewar sa, ta ceci kasar nan daga halin ha’ula’i. Wannan babban Malami yace yana cikin wadanda su ka fara nunawa Goodluck Jonathan cewa zai iya fadi zabe tun kafin 2015.

Ramas Azuzu yace shugaba Muhammadu Buhari yayi kokarin wajen maganin cin hanci da satar dukiyar gwamnati a Najeriya. Faston yace duk da shi rikakken ‘Dan PDP ne, amma an nuna masa cewa Buhari ne zai lashe zaben bana.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng